Hausa Novels Raina Kama Book 3 Hausa Novel

Raina Kama Book 3 Page 16


Raina Kama Book 3 Page 16
Viral

BOOK 3 ????1?6?

……………..Jin tsayuwar motoci ya saka Ameer lek’awa ta window, juyowa yay ya kalli Galadima, “Ranka ya dad’e y’an sandane”.
Baki Galadima ya ta6e, ya share tamkarma baijiba, yana cigaba da bud’e wasu file daya fiddo a briefcase. Saida yaja kusan 1 minute sannan ya mik’ama Nuren dake kusa dashi wasu files, ya zaro takarda kuma yay rubutun dabai Gaza layi biyarba ya mik’ama Ameer da wata k’amar waya a kwali.
Kar6a Ameer yazo yayi, batareda Galadima yayi magana ba ya nuna masa window.
Muftahu daya fahimta yace, “Ameer ka jefa musu takardan da wayan”.
Ameer ya amsa da to, yanufi window d’in, cikin dabara ya jefa kwalin da takardar.
Wani d’ansanda dayaga tahowarsu yay saurin zuwa kusada window d’in, ALLAH yabashi nasarar cafewa.
D.p.o dake tsaye tare da sauran police ana shawarar yanda za’a shiga gidan ya kaimawa.
Yay salute nasu kafin ya Isar da sak’on dukda yasan duk sunga daga ina kayan suka fito, d.p.o ya gyara tsayuwarsa yana fad’in “bud’e kwalin mu gani”.
Bud’ewa yayi, yaciro wayar yana cewa, “wayace sir”.
Cikin ta6e baki d.p.o ya jinjina kansa, yace, “takardar fa?”.
Itama bud’ewa yayi, yafara karanto abinda ke jiki, wanda Galadima ya rubuta da harshen nasara.

Kamar yanda suka fad’a Muhammad Sameer ba d’an ta’adda baneba, inhar zakubi yanda nace lallai yarannan zasu fita lafiya, idan kuma har kuka nuna k’arfin iko, zanta jeho muku gawarsu d’aya bayan d’aya ta saman benenan, ga wayanan, idan kuna buk’atar magana koni ina buk’ata ta wadatar, Dan kar wani yay gigin cewa zai shigo. Idan nayi ba dai-daiba a gafarceni????

Daga d.p.o har jama’ar dake kusa dashi duk ajiyar zuciya suka sauke, ya jinjina kai yana cije bakin mamaki, cikin sauke numfashi yace, “saimu bishi yanda yakeso mugani, idan munga zai mana wasa da hankali sai a d’auki mataki, C.. babangida a zagaye gidan”.
“Ok sir”. C babangida ya amsa yana salute nashi.
Dandanan suka warware wani blue d’in zare suka zagaye gidan dashi, mutanen anguwa dasuka fara fahimta harsun fara taruwa kallo, harma wad’anda sukaji a labaran sunfara gangarowa anguwar damin ganema idonsu.

Duk abinda ke faruwa Galadima Na zaune k’afa d’aya kan d’aya yana kallo ta CCTV, sai famar buga pen yake saman la66ansa a hankali, suma dai su Muftahu dasu Harun suna kallon komai.

Kujera aka kawoma d.p.o ya zauna, dayake da sauran safiya babu maganar neman runfa ko umbrella.
Wayar d.p.o ya kar6a da kansa, dan case ne Na manya IG da kansa yakirashi, yakuma abbatar masa shima yana nan zuwa.
Shiru d.p.o yay yana bincikar wayar da Galadima ya aiko da ita, babu komai a cikinta sai Number guda d’aya, baice komaiba yaciro wayarsa yayma IG bayanin komai.
Daga can IG yafara fad’a, wai tayaya zasu saurareshi, bayan d’an ta addane, duk Wanda zai iya kidnapping aiko d’an ta’addane, kawai su nuna masa k’arfin iko wajen ku6tar da yaran.
Shidai d.p.o ya kwantar da murya cikin sigar lallashi yace, “Nidai Sir da ace za’abi ta tawa daminbishi a hankali, maybe akwai sak’on da yakeson isarwa, karfa mu manta shima d’an manyan mutanene, shikansa akwai sarauta mai daraja a kansa, ai mai martaba bazai ta6a jin dad’iba shima, tunda ya buk’aci dama mu bashi, idan munga batai manaba saimu d’auki mataki”.
IG yace, “shikenan, Ku kirashi muji miyake buk’ata, nima a had’a dukkan maganar da zakuyi dani naji komai, dukda munama hanyar isowa yanzunan”.
Cikeda farin ciki d.p.o yace, “ok sir”.
Duk kayan aikin dasuke buk’ata suma sun tanadesu, yayinda y’an jarida suka fara isowa wajen.
Shima C.P ma saigashi ya iso, duk suka k’ame wajen salute nashi har d.p.o.
Ya amsa musu cikin jinjina kai, sannan ya buk’aci jin mi’ake ciki?.
Bayani d.p.o d’in yamasa, shima ya gamsu da shawarar abi komai a sannu d’in.

Galadima ya murmusa yana lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya. Saboda dukkan wayar da d.p.o yay da IG a kunensa ne.
Sudai su Nuren sunyi jugum-jugum Dan son ganin minene shirin Galadima waine?, da har yaza6i fiddo kansa wa duniya a matsayin mai laifi?.

Kiran da C.P yayi da kansane ya shigo wayar Galadima bud’e ido yayi yana kallon su ta CCTV, sannan yay picking call d’in, shiru yay yak’i magana, saida C.P ya fara masa sallama sannan ya amsa.
C.P yace, “Ranka ya dad’e barka da safiya”.
Baki Galadima ya ta6e, ya amsa da “Barka dai”.
Gyara zama C.P yay yana kallon saman gidan, duk su Galadima suna ganinsa, yace, “Ranka ya dad’e muna saurarenka, ka fad’i buk’atar taka, inhar batafi k’arfinmu ba za’a biya maka insha ALLAH ”.
“Humm” Galadima ya fad’a yana mik’ewa tsaye, duka hannunsa Na zube cikin aljihu, dayake yana amsa call d’in ne da abin da ke kunnen sa.
Falon ya shiga zagayewa cikin takunnan nasa na k’asaita da izza, saikace namijin tantabara yana gwada gasar tafiya a gaban matarsa????.
Suko sai binsa da kallo suke tamkar wani magiji.
A hankali yace, “Buk’atata ta farko shine iyayen yarannan su fiddo Alhaji Auwal fharuk, idan sunyi haka lallai zakuji manufata kai tsaye batare dana ja muku raiba, Dan nima ina buk’atar hutu”.

C.P ya shiga jinjina kansa kawai yana sauraren Galadima da dukkan sauran police d’in dasuma sukeda alhakin jin komai ta hanyar abinda suka saka a kunne.
Bai k’ara komaiba ya yanke wayar, Yakoma mazauninsa ya zauna yana kallon yaran dasuma dukshi suke kallo, d’an murmusawa yayi yana d’aukar ruwan daya ajiye, saida ya bud’e murfin ya mik’ama Wanda yake kusa dashi.
Shima yay murmushi yana girgiza kai da fad’in “A’a ranka ya dad’e, Na gode”.
Galadima ya mik’ama sauran suma, amma duk sai sukace A’a, murmushi yayi yasaka kayansa a Baki yasha, yana kallon Harun daya zuba masa ido, rabi yasha ya mik’ama Harun sauran, amma saiya kauda kansa gefe, Galadima ya ta6e baki yana d’aga kafad’a alamar kaika Sani.
Sauran ruwan ya ajiye yana kuma kallon yaran, da hannu yakuma yima Na farko alamar yaya sunansa?.
Bai fahimtaba Dan haka ya kalli Na kusa dashi, sannan yakuma kallon Galadima yana nuna kansa da fad’in “Sunana wai?”.
Galadima ya jinjina kai yana lumshe idanu.
“Sunana Ahmad Bana bb gana”.
Galadima ya had’e yatsansa babba da manuniya???? alamar nice name.
Ahmad yace, “Thanks you sir”.
Na kusa dashi Galadima ya sake nunawa, shikuma yace, “Ahakam Balala”.
Shima jinjina Galadima ya masa, nakusa dashi kuma Gebirel Timothy, sai Nerh-nerh Bilkisu Mansur, Rahma Abdul-naseer, Yassar Mamman, Sulaiman sager sulaiman, Marcel Miracle.
Cikin murmushi Galadima yace, “Duk sunan y’an gayune daku”.
Gaba d’aya suka sanya dariya, banda Harun da Alhaji Darma, Harun yasan Galadima sosai, dama yanada tsokana idan yaso hakan, koda kai zakayi dariyar shi ya fuske kuwa.
Galadima Yakuma fad’in “Duk kun kammala Secondary schools ne?”.
Duk suka amsa da eh, kowa yashiga fad’a masa matsayin karatunsa da abinda suke karanta, dukda ba magana yakeba murmushinsa Na sakasu farin ciki…..

………….?

A can kuwa waje, police nata k’ullawa da kwancewa da jiran isowar IG, Dan yace su jirayi zuwansa.
Dukda Galadima yana hira da yaran hankalinsa nakan saurarensu ta abinda ke kunnensa.

Babu dad’ewa saiga IG ya iso, kar6ar wayar yayi da kansa bayan sungama salute nashi ya zauna, ya kuma kiran Galadima da kansa.
Galadima yay picking amma sai yak’i magana yanzunma, hakanne yasaka IG yin magana cikin takaici da fusata, “Kai bamason rainin hankali, kafad’i abinda kawai kakeso duka amaka kabasu yaransu”.
K’ala Galadima bai ceba ya yanke wayar.
Mamaki ya kama IG, C.P yace, “Sir dadai anyi hak’uri an musu magana kawai suma aji mizasu ce”.
Cikin matuk’ar takaici IG ya dangwarar da wayar yana huci da cire hular kansa, da hannu yayma C.P umarnin a kirasun.
Da Sauri Aka danna kiran wayar d’aya daga cikin su, dama duksun tattarune a waje d’aya, Dan haka ya saka Hans free duk sunaji.
C.P da kansa ya sanar musu buk’atar Galadima, kallon kallo aka dungayi, kowa ya kasa magana, Shidai C.P ya yanke wayar yana fad’in “nanda mintuna 10 zasu kira”.
Suna ganin C.P ya yanke wayar suka hau cecekuce da fad’in yaronan yagama raina musu hankali, kaza-kaza dai, wasu suna bada goyon bayan abadashi sai abi tawata hanyar a kar6i camera d’in saboda suna matuk’ar k’aunar yaransu, wasu kuma sunce kar’a sakeshi, Dan haka tamkar tonon sililine agaresu. Sundai kasa samun matsaya har 10minute’s ta cika C.P ya sake kira. Ba’a samu Wanda ya iya d’agawaba harta yanke…….

(**********)

Zuwa yanzu gidan su Munaya sunsan halin da’ake ciki game da Galadima dakuma maganar fitowar Abba, Dan y’an jarida nata yad’a komai live a gidajen redio da TV, ga masu d’auka a waya y’an gani da ido dasukazo suka kafa suka kuma tsare.
Kuka dai Munaya Na shansa, tayi wujigi-wujigi, miji da Uba duk suna cikin matsala, da k’yar inna ta bata tea tasha da kanta, yaranma sai an mata dole take shayar dasu, ta lafe jikin innarsu tanata hawaye daga ita har Munubiya, yaran sai innaro dasu mama rabi’a da sukazo gidan Tun farar safiya ke kula dasu.

A can gefe kuma Zarah da Siyama NATA zagayen d’akin Abba Dan son samun damar shigewa su d’auki camera??????.

**********

Alhaji Hallurune yabasu shawarar su d’auka kawai suce su k’arya ake musu Alhaji Auwal baya hannunsu.
Wannan shawarar sukabi, da Kansu suka kira C.P suka shaida masa. Sharri Galadima ke musu.
Galadima dakejin komai yayi murmushi kawai yana cizar lips. Laptop d’insa ya janyo yafara danne-danne.

Daga can C.P ya yanke wayar yana Neman izinin IG domin kiran Galadima shima.
IG ya bada izini zuciyarsa Na sakejin zafin Galadima da rainin wayonsa.

Saida ta kusa tsinkewa sannan Galadima yay picking, C.P ya sanar dashi amsar da suka bada.
Cikin murmushi mai sauti da har su C.P sukeji Galadima yace, “ga za6i biyunan, kodai su fad’i inda yake, kokuma su sakoshi, kokuma shi yasaki video d’in yanda suka saceshi”.
Jikin C.P fa kansa yafara sanyi, Dan yafara hango k’amshin gaskiyar Galadima.

Bindiga Galadima ya nuna Alhaji Darma da ita, yamasa alamar ya matso gabansa, jikin Alhaji Darma Na rawa ya matso, waya ya mik’a masa, sannan ya danna kiran su C.P yana fad’in a had’ashi dasu yanzunan.
Kallon IG C.P yayi, alamar neman izini, IG ya bada damar hakan. Dan danan aka had’a Galadima da su, bindigar hannunsa ya d’ora saman kan Ahmad, maimakon Alhaji Darma, jikin Ahmad yafara rawa, tuni yafara kuka saboda tsoro, tsawa Suka dakama Galadima daga can.
Ahmad daketa mazari ya sanya kuka yana fad’in “Dady please and please kubashi abinda yakeso Dan ALLAH, wlhy zai kasheni, wayyo daddy I love you so much”.

Tuni Alhaji Bana ya rikice jin muryar d’ansa, Galadima ya cire bindigar daga kan Ahmad ya harbata gefe, k’arar ta tsorata su Ahamad suka rikice da ihu.
Rud’ewa su Alhaji Bana sukayi, Dan azatonsu Galadima ya kashe Ahmad ne, su kansa su IG dake waje duk sun tsorata da tunanin ko Galadima ya harbi wanine a cikinsu.

Galadima yace, “idan Baku shirya sakinshiba zan kashe Na gaba kuma”.
A tare suka hau ihu kowa yana rige-rigen fad’in zasu saki Abba.
Galadima ya ta6e baki yana gimtse kiran.
Alhaji Bana dai ya suma tuni, saboda tunanin an kashe masa d’a. Saidai suka zuba masa ruwa ya farfad’o, kuka rurus yashiga musu yana kiran sunan Ahmad d’insa, Yakuma rikicewa lokacinda Hajiya Fannah Maman Ahmad ta kirashi. Kasa d’agawa yayi…….

**
Galadima yay kiran su IG yana fad’in “inhar suka nakasa Abba ko kawoshi da wani mummunan raune abakin ran d’aya daga cikin y’ay’ansu, Dan haka a matsayinsu Na police su gargad’esu.

***

Antura Police inda suka kwatanta aje a d’akko Abbansu Munaya.

A inda aka d’aukeshi suka iskeshi ajiye cikin mota a sume, haka suka d’akkoshi suka taho, kai tsaye asibiti aka wuce dashi domin duba lafiyarsa, dukda babu wani ciwo a jikinsa Na alamar duka sai fashewar baki da kumburin da fuskarta tayi shima bada wani yawa can sosaiba.
Galadima sunga komai a TV saboda nunawar da akeyi, hawayen da suka taho masa ya had’iye da k’yar yana sunkuyar dakai danma kar wani cikin yaran kosu Muftahu su fahimci wani Abu, saidai tuni Nuren and Muftahu da Harun sun fahimceshi, Dan sunsa halayyarsa duka, yana da tausayi ainun.
Ran Harun A 6ace yake akan bada Abba dasu Alhaji Mansur sukayi, zuciyarsa sai tafarfasa takeyi, gashi kuma a d’aure.

Galadima ya mik’e yana bada izinin kowa yaje yay alwala time d’in salla yayi.
Idan kuma anyi salla su Farhat su shiga kitchen nema musu abinci.
Wannan adalci Na Galadima yanata tasiri a zukatan yaran, harsu gebiral.
Duk yanda Galadima yace haka sukayi, har Harun dake d’aure saida aka kwanceshi bisa tsayawar Ameer kansa da bindiga yay alwala.
Koda su IG suka nemi yin magana da Galadima saiya jefa musu takardar yana sanar musu time d’in salla yayi, bazai sake saurarensuba sai yayi salla..
Dole sukabi yanda yakeso, suma kuma ya tunatar dasu abinda suka manta.

………………………..?

Bayan idar da salla da gama girkin su Farhat aka kawo abincin kowa ya d’ebi iya buk’atarsa, yanzuma Galadima bai Ciba, kwanciyarsama yayi cikin kujera ya lumshe ido.
Harun dai anji wahala anci yanzu????.

………………………..?

Tuni mazan gidan su Munaya suka d’unguma zuwa asibitin Dan duba halin da Abba yake ciki, matan dai da yaran an barsu a gida, sai innaro kawai data Dage sai taje aka tafi da ita.

………………………..?

Buk’ata ta biyu da Galadima ya kawo bayan idar da salla itace a tura jami’an tsaro suje subama iyalan Abba tsaro a gidansa, hakama a asibiti.
Babu musu IG yasaka C.P, shikuma CP yabama D.P.O Umarni, dandanan aka sanar da station d’in yankin su Munaya, aka kuma k’ara dawasu police d’in harda mata da zasu shiga cikin gida.

Munaya taji dad’in hakan da Galadima yayi, Dan a tsorace tale dama.
Dole kuma Zarah da Siyama suka nutsu, Dan Munaya k’ofar Abba taja zugar y’an uwanta suka shimfid’a tabarma sukayi zaman jugum-jugum d’in a can.??????.

********

https://2gnblog.blogspot.com/
A masarautar gagara badau kam babu abinda kakeji Na tashi sai k’ananun magana. Bayi da kuyangi, dogarai da y’an gidan, manya da yara, kowane hadimi burinsa yafara kaima sashen dayake gulma, sunyi gungu-gungu suna tayi, sai anga wani babba zai wuce saikiga an watse.

Mai martaba ya kira papi, dukda yasan shima yaga komai, bayan sun gaisa a mutunce irin gaisuwar d’a da uba, suka shiga tattauna abinda ke faruwa, papi yace, ya kirashi amma wayarsa a kashe, yakira Nuren ma shima waya a kashe, Dan yasan lallai a tare suke shuka wannan tsiyar.
Mai martaba yace, “To amma Abba kaga kuma yanzu ga surukin namu sun fiddo kamar yanda ya buk’ata. Ina ganin akwai wani Abu da Sameer keson ankarar da jama’a Wanda mu bamu San dashiba, nasan halin yaronnan yanada k’yawawan halaye ababen koyi……”.
Cikeda 6acin rai papi ya katse mai martaba, “Jalaludden komai k’yawun halin Muhammad a yanzu ba kowane zai gansu koya yarda dasuba, dukda inaji ajikina bawai ganganci ya sakashi yin hakanba, dama yanada hujja, amma miyakai Na kisa?, a labarai sun nuna ya kashe yaron Alhaji Bana, shin wannan halin mutanen kwaraine? Wannan hanyar dayabi fa bazata ta6a 6ullewa da shiba sai 6ata masa suna damu kanmu, daga fitowar maganarnan zuwa yanzu nasamu kira babu adadi”.
Mai martaba yace, “kayi hak’uri Abba. Insha ALLAH zan shirya naje wajen zuwa anjima kad’an”.
“Shikenan. Idan naga nima abin yayi tsamari zan taho”.
Sallama sukayi kowa yana jimami akan lamarin.

Tunda labari yakaima mama Fulani tashiga tafa hannu tana sallallami da fad’in “A lallai zai iya zai aika, yo wannan yaron mai ido a tsakar goshi, fitinanne zai 6atama masarautarmu suna akan wani banzan talakan surukinsa, akuwa yanda ya kashe d’an mutane shima kasheshi za’ayi, idan munan ya rainamu yanzu kam ya d’ebo ruwan dafa kansa, fand’ararre kawai gagararre”.
Haka taita k’ananan magana da jifan Galadima da munana.

Oho shi baimasan tanayiba???.

********

A asibiti likitoci sun Shiga bama Abba taimakon gaggawa, Dan ba’asan minene ya sumar da shiba, tunda babu wani alamar duka ko harbi ko makamancin wannan a jikinsa..

******

Suma police sun buk’aci Galadima ya basu gawar Ahmad.
Murmushi yay yana kallon Ahmad d’in dake zaune yana shan ruwa saboda tsoratar dayayi sosai ta harbin da Galadima yayi, har yanzu yakasa sakin jikinsa, salla ma da sukayi a d’arare yayita, yazata da gaske shid’in aka harba, saida Galadima yayma Saleem nunin abashi ruwa, Saleem yakawo ma Ahmad ruwa, a lokacinne ya farga da Ashe yanada rai bai mutuba????.
Ya kar6i ruwa kuwa jiki Na rawa ya shiga kwankwad’a idonsa akan Galadima dake masa murmushi, yana bama su IG amsa da fad’in “karku damu yalla6ai. Inada freight d’in dazan dunga saka gawarsu anan, bayan aiki ya kammala saisu d’auki y’ay’ansu sumusu sutura, idan kuma sunyi abinda nakeso kaga magana ta k’are, gawar Ahmad kawai ce a k’asa dai yanzun, sai idan ank’imin yanda nakesone za’a samu fiye da hakan dai”.
C.P ya jinjina kai yana gyara tsayuwa, idonsa nakan ginin, yace, “to miye buk’atarka ta gaba yanzu?, tunda gashi an maka ta farko ai”.
“Eh tabbas anmin, dukda dai ankawoshi ba’yanda Na soba”.
“amma ranka ya dad’e suma ai ankashe musu yaro d’aya”.
Gira Galadima ya shafa da d’an yatsa yana ta6e baki, “ito dakuma wannan Dan wannan fa, yanzu dai inaga buk’atata tagaba shine ku kama mutanen nan guda 11 dazan lissafo”.
“Muna saurarenka, dawa-dawa?”.
Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, cikin Nisawa ya gyara zamansa yana d’aukar takardar dake gabansa ya shiga lissafosu. “Alhaji Balala, Alhaji Bana baba gana, Alhaji Abdul-Naseer Nafi’u, William Solomon, Hajiya A’i Barnawa, Alhaji Sageer Sulaima Sulaiman, madam Victoria, Mansur Habibu Abu, Josaya bamma, Alhaji Mamman k’afur, Alhaji Halliru garba”.

Kallon kallo aka tsayayi tsakanin IG da sauran police, sai C.P ne yasamu k’arfin halin cewa “amma to Ranka ya dad’e akan wane dalili? Kasan dai bazai yuwu muje kama mutane babu dalilin komai damuka saniba”.
Wani muskilin murmushi Galadima yayi, ya kwantar da kansa jikin kujera yana lumshe ido da cije lips, “Dalilin ai a fili yake yalla6ai namu, bisa dalilin Samun Alhaji Auwal Fharuk a hannunsu mana, dan yakamata asan dalilin samunshi a hannunsu, miya musu? Mi suke nema a wajensa? Baniba nasan dukan jama’ar garima abinda sukeson ji kenan, kunsan dai bazan ajiye ayukan gabana da jiyyar mahaifina nazo Nigeria Na zauna Ina kama yaran mutane saboda rashin aikinyiba ai, aimin kokuma nakuma aika yaronsu biyu barzahu yanzunnan!!”. Galadima ya k’are maganar cikin tsawa da matsanancin fushi.
Tsawarsa saida ta kad’a hanjin yaran, hatta da Harun dasu Muftahu saida suka rumtse ido, suma haka police d’in dake sauraren Galadima.
IG ya mik’e daga zaunen dayake yashiga safa da marwa Na mamakin wannan lamari, sukan ai ansakasu a tsaka mai wuya, cikin tsakkiyar fad’an manya. C.P ya kira suka koma gefe suna tattaunawa.

……………………….?

A can kuwa hankalin su Alhaji Sageer ya kuma k’ololuwar tashi, Alhaji Mamman yace, “lallai yaronnan anyi tsinanne, dama wannan ranar Na ringa gudu tun boss nada rai (tanderu yake nufi), amma wasunmu sukace yaron bai Isa mana komaiba, gashinan rana tsaka yana Neman zame mana RAINA KAMA….”
“Yama zama ai, Dan gayya kawai muka fara gani yanzun”. ‘Hajia A’i ta fad’a a tsorace’.
Duk sun kasa zama waje d’aya, Miracle yace, “yanzu nan da mutuncinmu za’ace wai y’an sanda su kamamu a k’asarnan?, lallai yaronnan yataro March wlhy”.
“Kokuma mune muka taro March d’inba”. Alhaji Bana dayake cikin kukan mutuwar d’ansa yafad’a yana share hawayen.

………………………….?

IG sun yanke shwarar bin umarnin Galadima kawai, kodan tseratar da yaran, yad’anyi magana da manyan dake kusa dashi dukda shine Oga kwata-kwata, kowadai yabada goyon bayan a kamasun kawai.
Dan haka IG da kansa yay kiransu, Yakuma basu dama a girmamame akan sukai Kansu kawai station d’in dake kusa dasu, kodan rayukan yaransu, daga baya za’asan abunyi insha ALLAH”.
Galadima dake saurarensu a zuciyarsa yace, abinyi kuma ai saidai a prison.

Duk sunk’i amincewa, wasunsuma sai bak’ak’en magana suke fad’a.

waya Galadima ya jawo yana daddannawa, sannan yayma Marcel nuni yazo, Dan yaji babansa yafi kowa zak’ewa, jikin Marcel sai 6ari yakeyi, ahaka ya rarrafo gaban Galadima.
Galadima yace, “’Dauka wayarka anan”.
Jikin Marcel na rawa ya d’auka.
“Kira daddynka”.
Dandanan yay kiransa, bugu d’aya kuwa ya d’auka shima jiki yana 6ari, duk suma sukayi tsitt suna jiran mizaice.
Galadima ya d’orama Marcel binduga a tsakkiyar kai, ya juya idanunsa alamar yay magana.
Marcel ya sanya kuka saboda tsoro. Rikicewa daddynsa yayi yana tambayar mi aka masa? Badai yay musu komaiba ba ko?…..
Katseshi Galadima yayi da fad’in “Zandai yimasa, Dan kaima yanzu d’anka zai wuce Inda Na Alhaji Bana yatafi”.
“kai kai dakata please ka dakata, nidai Na yarda zan mik’a wuya, karka ta6amin yaro kaji Na rok’eka”.
Cire bindigar Galadima yay yana maida kunamar da fad’in “shawara mai k’yau, lallai kanason d’ankan nan, ka tambayi abokanka, Wanda bazai mik’a wuyanba saiya fad’a yanzun nan”.
“karka ta6a mana yara please, duk zamu mik’a wuya”.
Galadima ya tuntsire da dariyar da wanima zai iya rantsewa bai ta6a ganin yayiba, yace, OK, good dattijan k’asa, saina jiku acan”.

????ana shagali a Nigeria yau kam???????????????????????? amma Nigeria novel ba tamuba??.

Su Alhaji balala dai kam sun mik’a wuya, da Kansu suka kai Kansu police station mafi kusa, daga can suma d’aukesu zuwa inda IG yace.
Galadima yay hamdala ga ubangiji dukda bawai komai yagama kammaluwa bane, amma lallai an d’akko hanya.
Ya bada Umarnin tashi suyi sallar La’asar, kafin a dawo a cigaba da gashi??.

………………………………?

Bayan sun idar da salla C.P ya kira Galadima, suka shaida masa su Alhaji Bana suna hannunsu yanzu haka.
Galadima dake tsaye yace, “Alhmdllh, zuwa safiyar gobe kuma sai a kai case d’inmu Court, Dan inason komai yafarune cikin gaggawa ya k’are, bana son jan jiki a aiki”.
C.P ya kalli IG Dan jiran amsa.
Kai IG ya jinjina masa alamar za’ayi hakan.
C.P ya shaidama Galadima amsar IG.
Galadima yace, shikenan, shi yatashi daga aiki, saikuma safiyar gobe.
C.P zaiyi magana I.G ya dakatar dashi alamar ya barsa kawai.

Ta6e baki Galadima yayi yana yanke wayar, ya maida kallonsa gasu Muftahu da duk suna maidashi television, gira d’aya ya d’age musu, sukuma sukai masa jinjina????.
Kauda idonsa yayi ya maida ga yaran, yace, “yaya akwai mai buk’atar wanka ko barci?”.
Gaba d’aya suka amsa da duk suna buk’ata.

Kallon Ameer da Saleem yayi yabada Umarni da ido.

…………………………?

‘D’aya bayan d’aya suka dinga kaisu suna wanka, duk Wanda yagama sai abashi lemo, batare daya San miye acikiba saiya shanye, daga sha ko mintuna 3 basa k’arawa suke 6ingirewa barci??.

????ho Galadiman mu kasan takan tsiya, Zuma kenan, ga zak’i ga harbi??????, kaga Na Munaya baban triplets, bada kanka a sare kaje gida kacema su mama Fulani an k’illesa????????.

Da akazo kan Harun k’in tankawa yayi, Dan haka Galadima yace su barshi kawai, amma harsu Malam Saminu da Alhaji Darma su Farhat duk sunma Kansu gyad’ar dogo sunje sun mik’e zasu huta.

Nuren ya kalli Galadima cike da tausayi yace, “Brother kaima kad’anje ka huta mana”.
Murmushin gefen baki Galadima yayi, yajawo lap-top gabansa yana girgizama Nuren kai alamar a’a……………..???

 

 

 

 

ALLAH ka gafartama Iyayenmu??????

 

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply