Hausa Novels Raina Kama Book 3 Hausa Novel

Raina Kama Book 3 Page 11-12


Raina Kama Book 3 Page 11-12
Viral

BOOK 3 ????1?1??1?2?

………….Mintuna basufi 20 da gama kwalliyar ba saigasu Aiyaan sun shigo dad’an gudunsu, Munaya na cikin d’aki tak’i fitowa, wai kunyar su inna suganta da kwalliya takeyi.
Inna ta dakama su Aryaan tsawa saboda batason wannan gudun.
Nutsuwa duk sukayi.
Tace, “Gudun mi kukeyine?”.
Y’ar rige-rigen fad’a suka fara, kowa yana ture d’an uwansa akan shine zai fara fad’a, ana cikin haka Yaa Anas yay sallama.
Hayaniyar su Aiyaan ta hana aji, sai laraba ce ta farga dashi, shine Yakuma yimasu Aiyaan tsawa suka nutsu, kowa ya zauna gefe yana tura baki.
Yaa Anas ya gaishe da laraba da innarsu munaya, Munubiya ma ta gaisheshi, ya Amshi Ameen dake hannun inna yana fad’in “inna Yalla6ai Galadima ne fa agidan namu, gashi kuma duk su Abba basa nan, shine nace ko’a kawoshi nan ne”.
Inna tace, “A’a Anas, ai ba’ayi hakaba, bara na d’akko makullin d’akin Abbanku saika bud’e masa nan ya shiga”.
Anas yace, “to inna”.
Laraba dake taya Munubiya shirya su Amaturrahman tayi murmushi, a ranta tana yaba yawan karamci na ahalin Munaya, mutanene masu dattako da sanin darajar d’an Adam, shiyyasa kullum take kuma taya Galadima murna da samun tsatson wannan mutane…….
Tunaninta ya katse lokacin da inna tadawo da key ta bama Anas, Ameen ta kar6a a hannunsa shikuma ya fice.
Munubiya tace, “innarmu ajiye wannan ki k’arasa sama Abdurraheem kayan Dan ALLAH, sainaje na had’ama Abbansu abincin, nasan yanzu yayi”.
Inna ta harareta, “kai nifa kunma maidani Nanny d’inku, nizan ke muku hidimar y’ay’ane?”.
“please mana innarmu, basune masu kawo miki kaza kina ciba sannan kin tsufa”.
Laraba tayi dariya tana fad’in “Gaskiyarki kuwa Maman 2, ALLAH dai yaja da rai”.
Inna tace, “iya kema biyema shirmennan nata zakiyi?”.
Laraba takuma darawa tanama Abbdurrahman rawa.
Itadai Munubiya ta fice tabarsu, laraba na bama inna amsa.

Duk ina jiyosu daga d’aki, haka kawai sainakejin wani iri, yanzu dole ta gaban su Innarmu zanbi natafi wajensa? Na kalli kaina a mirror kunya ta kuma kamani, dukda Simple kwalliya Munubiya tamin nayi k’yau, dan d’aurin kaina ya zauna dak’yau, fuskata ta kuma nutsuwa, har rantsuwa tamin inhar na canja wani Abu saitayi 2weeks batamin maganaba, nasan kad’an kenan daga abinda Munu… Zata iya, shiyyasa dole na hak’ura na bari…..
Shigowar Munubiya yasani waigawa na kalleta, ta harareni tana matsowa tamin kallon tsaf, nasan sotake taga mina goge kona canja, ganin komai yana yanda tayishi saita kuma d’aukar soson hoda ta gyara, ta d’akko turare tana kuma fesamin, hannunta nai saurin rik’ewa ina 6ata fuska, “Wai Sweetheart bazaki barshi haka bane? Turaren nan har hawa kaifa yake, Ni wlhy kunyarma fita nakeyi”.
Munubiya ta fisge hannunta tana dariya da fad’in “to kibi ta k’ark’ashin k’asa kawai mana, kuma wlhy ki nutsu, idan yauma tsiwar zaki masa saiki bada himma, anacewa mutum Idan ya haihu yana hankali kedai bakiyiba, saima rashinsa kika k’aro, malama muje yana jiranki”.
Yanda kukasan na make Munubiya haka naji, amma saina k’yaleta, nima nasan ta hanyar da zanbi na rama, gyalen data samin a kafad’a nabi da kallo.
nace, “haba Munu, amma wannan d’an gyalen Dan ALLAH?”.
“Okay, wajen surukinki zakine? ALLAH ki kiyayeni”.
Baki na murgud’a mata.
Tace, “oho dai, kije kimasa kidawo ta cinyayyen lips, danba barinki zaiyiba”.
Juyawa nayi na kalleta, amma saita d’auke kai tamkar bama itace tayi maganarba. Nayi kwafa kawai muka fito.
ALLAH ya soni babu kowa a falo sai su Aiyaan, hakkane ya sakani sauke ajiyar zuciya nad’an saki jikina.

Gwaggon Haleematu dake kaikawo a kitchen da tsakar gida saboda itace ta kar6i girki tabimu da kallo, gulma nacin ranta, daga ni har Munubiya d’auke kai mukayi tamkar bamu gantaba, muka shige falon Abba da takalman Galadima heif cover milk ke a k’ofar.
K’amshin turarensa yafara amsa mana sallama, na shak’a na lumshe ido.
Hankalinsa nakan yaransa da duk suke jikinsa, yana sanye cikin milk d’in shadda harda hular zanna bukar itama milk da d’an kwalliyar Brown kad’an, sosai yamin k’yau amma saina d’auke kai tamkar banma gansa ba.
Munubiya tace, “To Abban 3 gatanan nakawo maka”.
Murmushi yayi, idonsa sanye cikin farin eyeglasses, cikin muryarnan tasa mai kama da anmasa dole yace, “Thanks you Auntynmu”.
Murmushi itama Munubiya tayi, ta jinjina masa kai ta juya zata fita, har takai k’ofa ya katseta da fad’in “Su twins rowarsu akemin?”.
Hannu ta saka ta dafe bakinta, saikuma ta janye tana cewa, “A’a Abban 3 zasuzo su gaida abbansu insha ALLAH”.
Baice komaiba sai murmushi daya sakeyi.
Ta harareni sannan ta fice, Nina ramawa nayi.

Koda Munubiya ta fice saiya kuma maida hankalinsa ga yaran ya shareni, abin yabani haushi, jinaima kamar na fice abina, amma na danne zuciyata na matsa gabansa. Wajen tiren abincin na durk’usa, na d’auki jug d’in zo6on na zuba a k’aramin cup, d’agowar da zanyi na kamashi yana kallona, amma saiya basar, baki na tura kad’an, na mik’a masa cup d’in.
Bai kar6aba, sai wani bina da kallo yake tundaga sama har k’asa, a raina nace rainin wayo.
Idonsa ya janye daga kaina, ya fara kwantar da yaran d’ai-d’ai a gefensa, saboda a doguwan kujera yake.
Saida ya gama nakuma mik’a masa cup d’in, hannuna ya had’a da kofin ya rik’e, na d’ago ido muka kalli juna, duksai na daburce, danya cire eyeglasses d’in, kamar mai koyan magana na had’o kalmomin gaisuwar da gyar.
Nace, “i…na..yini”.
Wani Munafukin murmushi yayi yana lumshe idanu, ya kuma bud’esu a kaina yana d’age girarsa d’aya da cizar lips, a hankali ya furta “ke matsoraciya Ce, miye na rikitar daga kallo uhmyim?”.
Idanuna nad’an juya nace, “Tab badai niba”.
Ya ta6e baki kad’an, idonsa akan hannunmu dake had’e waje d’aya akan kofin.
Nima saina kalli hannun, cikin sanyin muryar dabansan nayiba nace, “da sanyi fa”.
“Really?”.
Shiru nayi ban amsashiba, ya zame kofin a hankali, sannan ya koma jikin kujerar ya kwanta yana hard’e k’afafu.
6oyayyar ajiyar zuciya na sauke, bansan miyasa inhar Galadima zai kasance kusa dani daf irin haka koya kafeni da ido nake rikicewa ba, haka kawai sainaji jikina yana tsuma…
Yay wani luuu da idanu saboda ajiyar zuciyar da tayi, zo6on ya kai bakinsa ya kur6a kad’an, dad’insa ya sakashi lumshe idanu ya had’iye.
Da hannu yamin nuni da kujera, tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki na mik’e, harzan bar wajen naje ta nesa dashi saiya rik’o hannuna. Juyawa nai na kallesa, ya nunamin kujerar kusa dashi da ido cikin tsare gida.
Banida za6in daya wuce bin umarninsa, na zauna tamkar mai shirin guduwa da ance ar.
Zo6on yakuma sha yana kallona, kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru.
Ganin haka sai nace, “yaya jikin Abie? dasu Momma?”.
Yaji dad’in ganin ta damu da ahalinsa, ya ajiye kofin yana gyara zama, yace, “jikin Abie Alhmdllh munata k’ara ganin haske, duk since na gaidaki dak’yau”.
Nace, “ina amsawa”.
Daganan mukai shiru, kowa yana tattaunawa da zuciyarsa, Idan ka gammu saika d’auka wasu saurayi da budurwane, irin had’uwar farko d’innan??.
Abimda na fahimta dai kamar yana tattare da damuwa ma, nad’an kallesa ta gefen ido, idonsa nakan yaransa, nace, “Abinci fa?”.
Maido da kallonsa yay gareni, yad’an yamutsa fuska yana girgiza kai.
Kallonsa nayi, cikin marairaicewar da bansan nayiba nace, “please mana yalla6ai, yanzu haka bakaci komaiba ka fito gida”.
Wani Abu dabaisan miyeba yaji ya tsarga cikin kansa har zuwa tafin k’afa, idonsa k’yam akan Munaya ko k’yaftawa bayayi, itama gareta hakanne, ta zuba masa ido batare da ta shirya hakanba, sai tsantsar tausayinsa dayake hangowa cikin idanunta, hannunta ya kamo cikin nasa, yana fad’in “kinaso naci?”.
A sanyaye na jinjina masa kai alamar eh.
Murmushin gefen baki yayi, ya matsa hannunta kad’an, “indai kinason naci akwai sharad’i”.
Batareda nasan mi bakina ya fad’aba nace, “kafad’a kona miye na amince”.
Kansa ya jinjina yana janye hannunsa, ya gyara zamansa yana fuskantata sosai, akan la66a ya furta, “saidai idan zaki bani da kanki”.
Babu shiri na waro manyan idanuna ina dafe baki alamar mamaki, ya had’e fuska yana ta6e baki da kwantar da kansa jikin kujerar. Yace, “Ashe ba sokike nacinba, kuma yunwa nakeji”.
Harga ALLAH inason yaci, dan na fahimci yanada buk’atar abincin, amma yana azabtar da kansa saboda bai yarda yaci na kowaba amasarautarsu, idan kuma ya fito inhar ba birnin gayu yajeba bazai ta6a cin komaiba inba ruwa ba harya koma gida kuwa…
Na sauke ajiyar zuciya, idona cikeda kwalla nace “to amma…”
Idonsa ya bud’e ya d’agamin hannu, amma baice komaiba.
Nima ban sake yunk’urin cewa wani abunba, na sakko daga kujerar na durk’usa a k’asa ina bud’e kulolin.
Mamaki ya kamani, dan ganin masa, a ina Munubiya ta samo masa haka? A lokacin da tasan zaizo yayi k’arancin da har za’ayi Masa. ganin babu mai amsamin tambayar na zuba hud’u a plate d’in, na d’ago ido na kallesa, Ashe shima ni yake kallo, idanu ya lumshe alamun ya Isa. Nima saina jinjina kai, kwanon da zansa miya na d’akko, amma saiya rik’e hannuna yana girgiza kai, na kalli plate d’in masar sannan na d’ago Na kallesa, ya kad’amin kai.
Fahimtar mi yake nufi da nayi saina zuba miyar gefen masar, sannan na mik’e da nufin komawa inda na taso, tiren abincin ya janye gefe, ya jawo center teble d’in a gabansa sosai.
Kallon teble d’in nayi shima na kallesa, saiya d’auke idonsa, a yanda ya janyo teble d’in inhar na zauna dolene k’afafunmu suke gogar juna, amma ya zanyi tunda na d’auki alk’awari.
Zama nayi, na d’ora plate d’in saman cinyata, na d’ebo masar da spoon na nufi bakinsa, baki ya ta6e yana girgiza kai.
Na dafe kaina irin naga ta kaina d’innan, na kallesa a marairaice, “yalla6ai to ya kakeso nayi please?, kaifa kace zakaci”.
Da d’an yatsa ya nuna hannuna. Cikin mamaki nace, “da hannu?”.
Yanda tai maganar tana zaro ido saiya so bashi dariya, amma ya had’iye kayarsa.
“O ni Munaya naga ta kaina”. Nafad’a a hankali.
A ransa yace zadai ki gani yarinya.
Dole na mik’e nakuma wanko hannuna a bayin falon Abba, na dawo, gyalena na zame dole na shinfid’a masa saman cinya gudun karna 6ata masa kaya, na fara d’ibar masar kamar yanda yake buk’ata na nufi bakinsa, saida ya kama hannuna sannan ya k’arasa dashi cikin bakin, ALLAH sai da tsigar jikina ta tashi, amma na daure nakuma d’ibowa, haka naita bashi har ya cinye, na bashi nama ya girgiza kai, alama namasa a k’ara?. Da d’an yatsa ya nunamin wai d’aya, bud’e kular nayi na d’auka, sauran miyar plate d’in ta isa, zan gutsura ya rik’e hannuna, a mamakina sainaga ya d’an ja hannun rigarsa sama ya saka hannu a plate d’in, idanu na waro da bud’e baki Dan mamaki, sai kawai naji hannunsa cikin bakina ya sakamin masa, ya d’agamin gira d’aya damin alamar inci, tamkar sokuwa haka na shiga taunawa, harna had’iye idonsa nakan bakina, saida ya rage saura lauma d’aya ya dakata da bani, na ida d’aukar laumar k’arshen na saka masa nima, ina niyyar tashi na wanke hannu ya maidani zaune, hannun dana bashi ya kamo yana sud’ewa, salon dayake lashe miyar saiya haifarmin da kasala, na rumtse idona harya gama sannan ya sakarmin hannu. Nima saina kama nasan na tsotse sannan na mik’e, ina toilet zan wanke hannuna zan d’ibo shima nakawo ya wanke sai na jishi a bayana, juyowa nayi na kallesa, ya mik’amin hannunsa. Bance komaiba na kama na wanke masa, na zuba masa ruwa ya kuskure bakinsa. Nidai gaba d’aya mamaki dukya nemi halakani.
Koda muka fito ina niyyar komawa inda na fara zama sai naji an fisgoni, jikinsa na fad’a, bance komaiba dukda naji zafi. Shima baice uffanba.
Lallai akwai abinda ke damunsa da gaske, hannuna na d’ora a kan k’irjinsa saitin zuciyarsa, ya bud’e ido sosai yana kallon hannun nawa, cikin aro jarumta nace, “Autan Momma mike damunka wai?”.
Murmushin dabai shiryaba ya saki, ya kalleni ido cikin ido yana fad’in, “kin rainani ALLAH kuwa, wannan autan bazai bar bakinkiba dai ko?”.
Murmushi nayi mai sauti, har hak’orana na bayyana, na had’e hannayena a waje d’aya alamar ban hak’uri, cikin langa6e kai nace, “tuba nake to na tsakkiya nefa kai ashe”.
Rankwashi yamin a kai, na dafe wajen dukda d’ankwali yasa banji zafiba sosai, amma na 6ata fuska ina k’ak’alo hawayen k’arya.
Gira d’aya ya d’age yana kallona alamar yadai?.
Na tura baki gaba ina fad’in, “da zafifa”.
Murmushi yayi yana kauda idonsa yana kallon yaransa.
Na yunk’ura da nufin sauka a jikina amma ya rik’eni, ba tare da ya kalleniba yace, “yakamata kisan kin girma”.
Bakin na kuma tunzurawa nace, “hu’im ina nan a babyna wlhy”.
Shi kansa baisan k’aramar dariya ta kufce masaba, ya d’an dara yana girgiza kai da kallona.
Ganin ya fara sakin jikinsa saina kuma cewa “Please yalla6ai bakada lafiya ne?”.
Tafin Hannunsa ya sanya saman kumatuna, a hankali tamkar mai rad’a yace, “mikika gani?”.
Na d’an kuma kwantar da murya ina janye idona daga cikin nasa, “Ba komai, kawai yanayinka ne ya nuna”.
Baice komaiba ya matso da fuskarsa gab da tawa ya had’e bakinmu, dukda na tsorata kar wani ya shigo ya gammu haka na barsa, yayi yanda yake so inhar hakan zai kauda damuwar dake ransa, nidai fatana na cika alk’awarin dana d’aukarma Momma a duk sanda na gansa cikin damuwa.
Saida ya gaji da kansa sannan ya bari tareda rungumeni yana sauke ajiyar zuciya, muryarsa can k’asan mak’oshi yace, “haka kike son ganina”.
Kaina na girgiza masa, ya d’agoni da sauri yana kallona, yace, “to yaya?”.
Murmushi nayi nafad’a k’irjinsa ina 6oye fuskata saboda kunya, shima saiya saka hannuwansa ya zagayeni yana murmushin, a hakanla ya furta “Thanks”.
Bance komaiba, amma naji dad’i daya godemin.
Kiran wayarsa da akayi ya sakani tashi daga jikinsa, zan tashi gaba d’aya ya rik’eni, a haka yay picking call d’in, na fahimci da papi yake waya, dukda kakansa ne yanda yake magana cikeda tsantsar girmamawa saiya birgeni, Mai dawakai danaji yana ambata da bayanin d’ansa mai suna Badi ne yaja hankali na, tsaf na fahinci zancen dukda bansan mafariba, yakuma yanke maganar bai k’arasaba yana fad’ama papi sai yazo zasu k’arasa zancen.
Yanke wayar yayi yana huremin ido saboda kallonsa dana keyi, tunda ya fara wayar.
K’asa nayi da kaina dan naji kunya ya kamani ina kallonsa, ya ajiye wayar yana fad’in “Zamukai Abdurrahman asibiti ne?”.
Kaina na girgiza masa. nace, “A’a aiya warke bama sai an kaisa ba”.
Yace, “Okay”. Idonsa akan yaran, Abdurraheem ya fara motse-motsen tashi, sauka nayi a jikinsa nakoma gaban kujerar na durk’usa ina d’an bubbuga bayansa, dan banason ya tashi, inhar ya tashi saiyasha nono, sauran kuma suma duk tashi zasuyi, bada nono a gaban Galadima shine abinda nake gudu ni kuma.
Shikam tsura musu ido yayi cikeda sha’awa daga ita har yaran, ya d’auki wayarsa yamusu hoto batare da ta saniba.

Saida naga ya koma barci sannan Na dawo kujerar dana fara zama, shima zamansa yagyara yana kallona, magana yakeson yi amma yanata juyata a zuciya, nidai bance dashi komaiba, saida ya gama k’asaitarsa da basarwa sannan yace, “Abba fa?”.
Nace, “yayi tafiya yau kwana biyu”.
“zuwa ina kenan?”.
“wlhy ban saniba, amma miya faru?”.
Kansa ya girgizamin alamar babu komai, yad’an furzar da huci yana kallona agogon hannunsa. “Shikenan ni zan wuce, zan iya dawowa a kowane lokaci inhar Abba ya dawo”.
Kaina na jinjina masa, ya mik’e, nima saina mik’e ina fad’in “yaa Sauban fa?”.
Bai tankaminba saida ya duk’a yayma yaransa kisses a kumatu sannan ya d’an kalleni ya d’auke kansa, “Tare muka dawo, amma zai wuce masarautar su papi gobe, dan a can zai zauna harya gama”.
“ALLAH ya bada nasara”. Nafad’a ina sauke ajiyar zuciya.
A kan la66a ya amsa da amin.
Harya kusa nufar k’ofa nace, “bakace komai game da maganarmu bafa”.
Cak ya tsaya amma bai juyoba, a haka yace “wace magar?”.
Wani yawu na had’iye da k’yar ina fad’in, “Maganar rabuwa, nifa gaskiya bazan komaba”.
Saida yaja kusan seconds 20 kafin ya juyo yana fuskantata, kallon da yakemin yasani janye idona daga kallonsa, cikeda k’asaitarsa yatako ya dawo inda nake tsaye, hannayensa ya cusa cikin aljihu yay matuk’ar d’aure fuska, cikin izzarsa yace, “wai nikam miyasa kikeda naci?”.
Nima fuskar na tamke. Nace, “Neman y’ancina nake, tun farko a wannan tubalin ka gina auren, mizaisa kuma lokacin rugujeshi yayi bazakayi hakanba?”.
Lips d’insa ya ciza yana kallona da k’ank’ance idanu, cikin salon Basarwar tasa yace, “So what idan nine na gina a haka d’in? Kinsan dai bazaki ajiyemin yara ba koda abinda kikeson ya kasance, dan yarana bazasu sha madaraba bayan sunada abinci”.
“Humm” na fad’a cikin takaici. na gyara tsayuwa idona na cikowa da kwalla, “Yalla6ai karka manta a randa na kwana biyu gidanka da bakiknka ka tabbatar min baka zalunci? daga ni har kai mun amince cikin yarannan ya zone cikin k’addarar dabamu shiryama zuwanta ba, to mizaisa kuma zuwansu duniya yazama salon tauye hak’k’ina? Na amintane da aurenka domin warware k’ullun da akaimin da wanda yake kan mahaifina, bawai dan bansan y’ancin kainaba ko darajata, idan har nice a matsayin Amaturrahman zakaso wani ya aureni a matsayin auren shekara d’aya ko biyu domin cikar wani burinsa ya rabu dani?, addininmu da al’adarmu duk basu koyar damu hakaba, anayin aurene domin ibada, saboda bautar ALLAH ne, sannan ana ginashine bisa tausayi da rahama, inhar zuciyarka bazatayi dad’iba a matsayinka na mahaifin Amaturrahman idan hakan ace akanta ta kasance, to ya kake tunanin randa nawa mahaifin yasan gaskiyar matsayin nawa auren zaiji?, tunda nataso nake d’and’anar zafi da d’aci na zamantakewar rayuwar gidan yawa, taya zanso saka rayuwata a walagigin kila wa kala, na shigo wannan yak’inne domin neman y’ancin kai badan ribantuwa da ganima ba, amma lokacin dana wayi gari da abinda ban shiryamawa ba a cikin jikina haka na hak’ura na kar6a da hannu biyu saboda k’ok’arin cinye jarabawa, miyasa kakeson yin wasa da rayuwatane wai? Duk motsi dai yaranka! Yaranka! Karka manta nimafa y’ar wasuce, kamar yanda kakeji haka suma sukeji akaina, inason nima nayi aure na zauna tamkar kowacce mace a gidan mijinta, na fidda hak’insa da ALLAH ya wajabta min, shima ya fidda min nawa da ALLAH ya wajabta masa……”.
Hannu ya d’agamin alamar ya isheshi haka, yakuma matsowa gabana cikeda izza yace, “mikikeso yanzun?”.
Nace, “sanin matsayin aurena, inhar yaranka ne zan muku sadakar shayarwa na wata shida na yayesu nayi aurena da mijin dazai soni ya k’aunaceni domin ALLAH”.
Bakinsa ya ta6e yana cije lips, jijiyoyin kansa duksun mimmk’e saboda 6acin rai, cikin takaici yace, “Yarinya har abada babu shegen namijin daya Isa na k’etara gona shima ya k’etarata, koda kuwa wannan gonar ta jinginace, ko ayanzu nabar duniya wani yayi hakan ban yafeba, duk gonar dana ra6a tawace ni kad’ai koda banyi noma a cikinta ba, wannan yazama first and last da zaki kuma kawomin irin wannan maganar, kodan kinga ina k’yaleki ne shiyyasa kike d’aukata wani sauna kiringa min zancen wani banza can daban, Munaya karki yarda na nuna miki a salin true color d’ina wlhy, ina kuma gargad’arki a karo na k’arshe”. ‘ya k’are maganar da bugamin yatsunsa biyu saitin fuska ya fice abinsa’.

Baki na ta6e ina bin inda yabi da harara, sannan na saka gyalena na goge hawayen dake zarya a kumatuna nai kwafa na fice abina nima nabar yaran.

 

**********

Tunda ya fito Muftahu ke binsa da kallo, harya bud’e mota ya shiga baiko kalli Muftahun ba shi.
Dama shine ya kawoshi, amma yana ajiyeshi ya koma saboda wani aiki daya bashi, dawowarsa kenan yana k’ok’arin kiransa yace zai shigo su gaisa da Munaya shine yafito a fusace.
Baice dashi uffanba ya bud’e motar shima ya shiga ya tada suka tafi, saida sukayi nisa da tafiya sannan Muftahu yace, “Ranka ya dad’e wai mike faruwane?”.
Shiru yamasa yak’i tankawa, shima Muftahu sai yaja bakinsa ya kulle ya cigaba tuk’insa.
Sai jera tagwayen tsaki yakeyi, Muftahu ya kuma kallonsa sannan ya maida hankali ga tuk’insa, ya kuma rik’e sitiyarin yana fad’in “ALLAH ya huci zuciyarka ranka ya dad’e, idan kana ganin bazaka juri zuwanba kace ta dawo mana kawai”.
Cikin jan wani tsakin yace, “inhar taci gaba damin zancen wani wawa lallai zan datse harshenta wataran”.
6oyayyan murmushi Muftahu yayi, a zuciyarsa yana jero hamdala wa ubangiji, dan babu abinda yake hange tattare da galadima sai tsantsar kishin matarsa, dukda baisan miya had’asuba yaji dad’in hakan, koba komai yanzu ya fita daga damuwa da fargabar rabuwar wannan auren. cikin son kuma fahimtar wani Abu yace, “to amma ranka ya dad’e yazamuyi idan lokacin rabuwarku yayi kenan? Kasanfa alk’awarin da mukai mata”.
“Oho! Maka”. Galadima ya fad’a cikin tsananin fusata.
Da k’yar Muftahu ya iya had’iye dariyarsa, bai sake cewa komaiba har suka isa gidan baffi, dan karya mazgeshi a banza. Muftahu ya fita domin nema masa ison shiga ciki, a lokacinne yasamu yay dariyarsa mai isarsa, lallai Galadima akwai kishi, tashin hankali, irin wannan ajiyar zuciya haka.

 

*********

Tunda na shiga Munubiya take bina da kallo, ta ce, “ina yaran?”.
“Suna can”. ‘nafad’a ina shigewata ciki’.
K’ala bata sake cewaba tafita abinta.

Har dare ina fushi, nak’i kula kowa, innarmu yitai kamarma batasan inayiba, dukda batasan mike damunaba, Munubiya ma shareni tayi, sai laraba Ce ke tambayata kodai banajin dad’ine?, nace a’a.

__________

Saida Muftahu ya raka Galadima har falon Baffi sannan yace zaije ya dawo kafin su gama.
kansa kawai ya d’aga masa amma bai tankaba.
Fitar Muftahu babu dad’ewa baffi ya fito shima, zama yay idonsa akan Galadima, dan ganinsa cikin damuwa, “d’an baffi miya farune haka?”.
Galadima yafara k’ok’arin saita kansa cikin k’ak’aro murmushi yace, “Babu komai Baffi”.
Duk da bai gamsu ba saiya k’yaleshi, dan maybe ba huruminsa baneba, yace “Alhaji Rabilu yakai maka bak’o ko?”.
“Eh d’azunnan muka rabu dasu, abindama ya kawoni kenan, dan ina ganin insha ALLAH mun sami dukkan bakin zaren, zan fara aikina kawai”.
Murmushi baffi yayi yana gyara zamansa, yace, “eh to ansami bakin zare kuma ba’a samuba, dan yanzu binciko Wanda Camera d’in take hannunsa shine babban aikin dake gabanmu, dan itace babbar hujjarmu bayan d’unbin hujjoji da muke dasu a k’asa”.
Galadima ya sauke ajiyar zuciya yana jinjina kai, “hakane Baffi, amma akwai dai wasu y’an bayanai danake dasu a hannu yanzu haka, sai dai banida tabbacin dai-dai ne? Kokuwa akasin haka, amma kama SD da mukayi shine zai fito da gaskiyar hasashen nawa”.
“To shikenan, ALLAH yasa muji alkairi”.
“Amin, saidai ni a bayanin Baba Rabilu akwai abinda har yanzu yakemin rawa a zuciya”.
“tofa, minene kenan?”.
“Maganar siyasa dayacemin ya shiga a wancan shekarun, bayan kuma lokacin mulkin sojane, kenan wace siyasa sukayi?”.
Baffi yay murmushi, “wato abinda na fuskanta anan shine, yasako kalmar siyasa ne domin mu mufasa sauran bak’in da kanmu, amma tabbas a wancan lokacin babu wata jam’iyyar siyasa, wayema ya Isa d’aga murya akan mulkine? Saidai bincikena ya nuna Dalilin kafa Group nasu tanderu yanada nasaba da son kafa mulkin farar hula, wato sunason mulki yabar hannun sojoji kenan, saidai a 6oye sukeyin dukkan abinsu, har suka ringa jawo ra’ayin mutane mabanbanta a cikin tafiyar tasu, abinda na kasa fahimta nima shine, shin sunjawo Alhaji Rabilu ne dansu tabbatar Camera na hannunsa? Kokuwa shine yakai kansa garesu domin lek’en asiri? Dole cikin biyunnan a samu d’aya, kodan yunk’urin kasheshi da suka saka Darma yayi”.
Galadima dayay shiru yana fassara zancen Baffi dak’i-daki ya shiga jinjina kansa alamar gamsuwa da bayaninsa, zuwa can yace, “Baffi ka bani kwanaki biyu zanyi bincike insha ALLAH, dan zan tattauna da SD da kuma Harun, sannan akwai yaron da aka saka yay aikin da aka buga a jaridarnan, shima inason yazo hannuna insha ALLAH ”.
“ALLAH ya cigaba da dafa maka, Yakuma tsareka da dukkan sharri, lallai ka ringa kulawa, dan yanzu dukkan wata hanya da zasubi domin cuta maka sun tanadeta, karka d’auka suma basa bibiyar lamarinka kamar yanda kake bibiyar nasu, dan ranar naga Alhaji Abdul- Naseer da wani masanin Computer, saidai shi bai ganniba, nasha jinin jikina kwarai da gaske, amma nikam inamason tambayarka, minene alak’ar Surukinka da senator halluru ne?”.
“kamar dai abokinsa ne baffi”.
“Ok! Ok! To lallai ka sanar masa ya lura, dan Senator Halluru yaronsu tanderune, za’a iya bi ta hanyar surukinka a 6ata mana aiki, tunda sun san akwai alak’a tsakanin kai da shi”.
“wannan gaskiyane Baffi”.
Sun cigaba da tattaunawa akan matsalolin da ayanzu zasu fuskanta, baffi na kuma bama Galadima dabaru a shara’ance Wanda bazai aikata abinda shima zai rufta ba.

Sai dare ya koma masarauta, yinin yau gaba d’aya a tsaye yayisa, shiyyasa duk jikinsa ciwo yake masa, yanayin zirga-zirga amma ba irin wannanba mai cikeda cajin kwakwalwa da rikitar tunani. Ga maganganun Munaya dake cin ransa, ya tabbata duk gaskiya ta fad’a, hakan datake yana kuma tabbatar masa da tasan darajar kanta, inda watace shiru zatayi sai yanda yaso yi da ita, duk kuma abinda zai mata koda Mara k’yaune zata shanye saboda kasancewarsa d’an wani, amma duk da kasantuwarta mace kuma wadda take k’ark’ashin mulkinsu ALLAH bai sakama zuciyarta tsoro ko kwad’ayi ba, itadai kullum burinta shine asan darajarta da kimar ahalinta, sa6anin y’an matan yanzu da duniyar Ce kawai burinsu da son ganinta a tafin hannunsu, auren mai kud’i ko mulki, mai k’yau ajin farko, na nunama k’awaye da yin alfahari a duniya, yasan darajarta kona iyayenta wannan ba matsalarta bace, yanada addini ko kula da addinin shiyya Sani, son gaskiya yake mata ko albarkatun jikinta yakeso batada matsala, ya zube a kujera yana sauke tagwayen numfashi.
Sauban dake zaune yana kallo yakuma kallonsa, yayansu na bashi tausayi, saidai shi taurinkai da rashin yarda da kowansa ke had’ashi dashi, amma ta wani fannin yakan kalli hakan a matsayin gaskiyarsa, dan massarautar tasuce abar tsoro, ba kowane abin yardaba, yanda zaka tantance na kirkin shine mai wahalar kuma.

*******

Na kasa hak’uri da danne maganganun Galadima, hakanne ya sakani yanke shawarar tambayar Munubiya kota Sani, saida mukai shirin barci dukda sharenin da takeyi nadai danne nawa Fushin na zauna kusa da ita tana shayar da Meenat data tashi. Kan yarinyar na shafa sannan nace “Munubiya in tambayeki mana please?”.
Kamar bazata kulaniba sai kuma ta kalleni. Tace, “Ina saurarenki”.
Ajiyar zuciya nayi ina gyara zamana, nace, “dan ALLAH idan namiji yace gonarsa mi yake nufi?”.
Jimm tayi alamar tunani, ta kwantar da meenat tana fad’in “Matarsa”.
Da mamaki na kalleta, yayinda wani sanyi ya ratsa raina, amma na danne…….
Ta katseni da fad’in “Munaya ki fito fili ki sanarmin abinda ke faruwa, kinsan banason kwana-kwana, sirrinki keda mijinkine kawai a rayuwa bazanso saniba, domin ALLAH ya haramta bud’e wannan, saikuma yankin sirrinsa na rayuwa Wanda yarda da matarsane kawai zaisa ya fad’a mata, shima wannan kirik’e masashi, amma Munaya na fuskanci har yanzu babu dai-daito tsakaninki da mijinki, duk da kin sanarmin da manufar aurenku nazata darajar zuri’ar data shigo tsakkiyarku zai kawo muku sasanci Ku manta da wani auren Contract, duk da na fahimci mijinki jinin mulki na yawo a jikinsa, danne Abu a rai da basar dashi tamkar jinin jikinsa yake, kekam nasan halinki mutumce maison a damu da ita, sannan a nuna mata komai a aikace da furucin baki, kema danaki jinkan Wanda bansan gidan uwarwa kika samoshiba, amma mike wakana a duniyar aurenki? Mikuma kuke shiryawa keda surukarki?”.
Shiru nayi nakasa magana, dan banso fitar da wannan sirrinba har zuwa lokacin da Momma ta bani, duk da nima rashin sanarma y’ar uwata yana damuna, dan bamu ta6a 6oyema juna wani abuba, ko akan aurena daga baya kasa daurewa nayi na sanarmata, duk da na 6oye matanne saboda gargad’in da baba mai kanwa yamin……
Kwanciyarta tayi tana cewa, “idan kinga bazaki iya fad’aba kibar abinki arai yayta cinki, daga k’arshe idan kika rufta auren ya tsinke kekika Sani, kinsandai minene wannan gidan da irin mutanenen cikinsa, dama kullum burunsu kenan”.
Idona cike da kwalla na kamo hannunta, “kiyi hak’uri sweetheart tashi muyi magana”.
Munubiya taiyi kamar ta shareta saikuma ta tashi tana share mata hawayen dake bin fuskarta.
Ta gyara zamanta tana fad’in “wato Munubiya……………..?????

 

Kumuje zuwa page nagaba my guys????.

 

 

 

ALLAH ya gafartama iyayenmu??????

 

 

ALLAH ya gafartama iyayenmu??????

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply