Hausa Novels Raina Kama Book 2 Hausa Novel

Raina Kama Book 2 Page 9


Raina Kama Book 2 Page 9
Viral

Book 2~ ????9?

……………..Salon nasa yasani bashi ragama, dan Galadima yazo min da sabon salo mai tafiya da gudun jini dana zuciya.
Duk da kasancewata farin shiga, hakan bai hanani gane Galadima Na daban bane, kamar yanda kuka sanshi mutum mai izza da k’asaita, hakan bai canja ba ta wannan fanin, komansa a nurse da izzar k’asaita yake gudanar dashi. ban tashi farga nayi kuskure ba saida labari yafara nisan zango, anzo wajenda tsorosa yafara tasiri a gareni, Sai dai kuma nayi sakacin da Galadima yazama kurman dutsen dabaya ji baya gani. Sai lokacin hawaye suka fara ambaliya ga fuskata, hannayena na k’ok’arin d’agawa domin rok’o, sai dai ya hanani wannan damar gaba d’aya……….

??????kai babu ruwana, iya nan nagani nima?? aradu aunty Magajiya da aunty Ni’ima zasuci k’aniyata ne idan na k’arasa fad’a???????????????????.

Tabbas na gurzu, dan yau na banbance tsakanin aya da tsakkuwa, banbancin baya cikin hayyacinsa da yau d’inma kad’anne, dukda babu yanda za’ayi daren farko yayi dai-dai da kowacce rana ta bayansa.
Duk ajiyar zuciyar danake saukewa yana jina, amma yay luf a gefena, hakan ne Yakuma tunzurani, a zalinceka akasa lallashinka saboda jin kai, wlhy kasaitar bawannan tayi masa yawa, duk randa yazama sarki kam fadawa sunga takansu, dan magana dai idan sarki na uku a fada toshi bazaiyi ko guda d’aya ba??.
Galadima daduk yake sauraren kukan nata da ajiyar zuciya ya juyo kad’an yana fuskantarta, hannu yasaka ya tallafo fuskarta ta matso dai-dai da tasa, jinai kawai ana huramin iska saman ido, tsaf na fahimmci iskar bakinsa yake huramin, amma saina dake nak’i bud’e idona.
Muryarsa can k’asan mak’oshi ya furta “my friend are you okay?”.
Banza na masa, nakuma k’i bud’e odon, lallai mutuminnan yacika d’an latsin rainin wayo number 1, yanzunan Galadima har yanada bakin yimin wannan banzar tambayar?, idona a rufe har yanzu na bud’e baki cikin salon tsiwa zan maka masa bak’ar magana, amma saiya d’ora yatsansa saman bakina yana fad’in “shiiii!??” da bakinsa, shirun kuwa nayi kamar an rufemin bakin Dan Nina Na tuna illar yin tsiwar.(????)
Ya matso dani jikinsa ya rungume, hannunsa na buga gadon bayana k’ad’an-k’ad’an, ya d’ora bakinsa saitin kunnena, “yanzu kin gane banbancin Sameer da Munaya right?, idan kuma har yanzu baki fahimta ba to bakinki ya cigaba d’amin tsiwa OK?, nikuma bazan gaji da punishment nashi ba sala-sala yalla6iya??”. ‘ya k’are maganar da sumbatar cikin kunnena’.
Babu shiri na k’ank’amesa dan har cikin kwalwar kaina naji sumbar nan.
Kad’an ya buga bayana sannan ya janyeni daga jikinsa ya sauka daga saman gadon.
“hasbinallahu wani’imal wakil” na iya maimaitawa kawai, na k’ank’ame pillows d’in gabana ina rintse idanu da cije lips (copy copy??).

Kusan mintuna 15 duk nazata yama fitane, sai kawai jinai an d’aukeni. a razane na bud’e idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, da matuk’ar Sauri na maida nawa na lumshe.
Wani muskilin murmushi Galadima yayi yana cije lips.
Ba shiri na bud’e ido, saboda jina cikin ruwan zafi, yunk’urawa nayi zan mik’e cikin 6ata fuska ya maidani ya zaunar yana fad’in “za6i ya rage naki, zama kiyi da kanki, kokuma ni nayi miki..”
Banma bari yakai k’arsheba na koma na zauna ina kare k’urjina.
Kafad’a ya d’age sama yana ta6e baki da fad’in “hummm”.
Fita yay daga bathroom d’in ya rufe mata K’ofar.

Na kai tsawon lokaci a bayin ina Gasa jikina, dan nasan idanma banyiba kaina nama mugunta, saida naji ko ina ya saki sannan nayi wankan tsarki ina hawaye, bansan yanda zan fassara wannan muguntar ta Galadima ba kuma, wannan karon kuma tsautsayin zaice kokuwa ba yin Kansa bane?.
Haka dai na kammala na d’aura towel d’ina, a zuciyata ina addu’ar ALLAH dai yasa ya fita, dan towel d’in guntune, bai gama rufe cinyoyina bama baki d’aya.
Da sand’a na fito, yauma inajin zafi kad’an-kad’an, amma ba kamar na ranar ba. ganin baya d’akin saina ida rufe k’ofar na tako cikin d’akin sosai.
Ina neman kaya a wardrobe ina share hawaye, indai rashin tsiwar dayake fad’ace na daina masa, dan bazan zauna ya illatani a banza ba, wannan k’addararren cikinma daya hanamin gangar jiki hutawa da ciwuka ya isheni, basai na cigaba da 6alloma kaina wata muguntar tasa ba.
wata ‘yar riga mai d’an nauyi-nauyi na samo, na cirota dan sanyi nakeji, juyowar da zanyi saina gansa zaune bakin gado yana danna laptop, hannunsa d’aya rik’e da glass cup yana shan fresh milk hankali kwance.
Saida nad’anja baya, nakuma bud’e rigar ina kare jikina.
Duk abinda takeyi yana kallonta ta gefen ido, amma yawani share kamar baima San da itaba.
Da bin bango da sand’a na koma bayin, ta gaba kuma ina karewa da rigar.
Saida ta shige ya d’ago kai yana kallon k’ofar bayin, saikuma ya girgiza kai yana murmushin gefen baki. cigaba yayi da aikinsa a nutse.
Barci nakeji, ga zazza6i yafara rufeni, hakan yasa ina gama saka rigar na fito, naci serious kawai sannan na fito.
d’ago idanu yayi muka had’a ido, da sauri nad’an rankwafa inajan rigar barcin k’asa wai danta rufemin cinya zuwa kwauri.
Baki ya ta6e yana wani janye ido cikeda basarwa. Irin shi baiga abin kallo d’in nanba.
Ni kuma na dalla masa Harara ina k’ok’arin hayewa gadon.
“ji mana”. ‘yafad’a cikin izza’.
Banza na masa zan haye gadon.
Yace “iyim, bakije daddarawa ba kenan yarinya, saina sake kaiki yanzunnan….”.
Kafin ya rufe baki nama iso gabansa na tsaya.
d’agowa yayi yana kallona yana kur6ar fresh milk nashi, ya d’agamin gira d’aya.
Baki na turo masa ina share hawaye.
Ya kamo hannuna ya zaunar kusa da shi, “nikam yalla6iya karki haifomin abin cikin kwan da halin kuka, bana son ragwan taka, ‘yata ko macece jaruma za’ayi, irin wadda labarinta zai zaga lungu da sak’o na duniya”.
Harara na balla masa, yay saurin rik’e cup d’in hannunsa dayake zuba frash milk a ciki, “eh me, malama karkisa hantar cikina fitowa, irin wannan harara haka”.
Kad’an yarage banyi dariya ba, da gaskiyar Momma, halin Galadima d’aya da Sauban, tsantsar harmutsine da sanya damuwa a rai ya lullu6e halinsa na barkwanci, hakan kuma yanada nasaba da rashin samun mai jansa a jiki yana d’auke masa kewa da rage masa rad’ad’in damuwarsa. Momma hankalinta nakan jiyyar Abie, Aunty mimi kuma rainon Sauban, mom kuma tayi aure lokacin dayake buk’atar makusanci, s…….
Firgigit nayi saboda hancina da yaja, na kalleshi ina tura baki.
“maida wuk’ar yalla6iya, abin bana fusata bane, wace duniyar kika tafi hakane da nisa inata magana?”.
Marairaice fuska nayi ina shirin fara kuka, “please ka barni na kwanta barci nakeji”.
Kofin hannunsa ya mik’amin, na waro idanu ina girgiza masa hannu alamar a’a”.
Shima saiya waro nasa idanun yana fad’in “why?”.
“kawai ni bazan sha bane, aje a zubamin wani abu”.
“hakane kuma”. ‘ya fad’am yana kamoni ya jawoni jikinsa’.
Saman cinyarsa na zauna, da hanzari nafara k’ok’arin mik’ewa. shima saiya kama hannayena ya maidasu baya yanda bazan iya kata6us ba, madarar ya d’auka ya guntsa da yawa a bakinsa.
Waro idanu nayi ganin ya nufo bakina gadan-gadan, duk yanda naso kauda fuskata ya gagara, na datse hakwarana da sauri, shi kuma saya toshemin hanci, hakan yasa ni bud’e baki dole, dan ina buk’atar shak’ar numfashi. Tas ya juyemin fresh milk d’in abakina, sannan ya kuma rufe hancina saida na shanyeta sannan ya janye bakin, ni dashi duk muka hau sauke numfashi, kuka na sanya masa, amma hakan bai hanashi kuma guntsar madarba ya kuma juyemin a baki na, haka yayta min, ya kuma k’ara rabin kofi kuma, saida yaga ta kwalin ta k’are sannan ya sakarmin hannu na tashi zaune.
Bansan kawai na fara kaima k’urjinsa k’ananun dukaba, ina fad’in wlhy sai ALLAH ya sakamin, kai bama zan yarda ba fa, saboda k’azanta kaita had’a yawunka da fresh milk kana d’uramin, ni bazan yardaba”.
Shagala kawai yayi yana kallona, yakasa kare kanshi balle yunk’urin hanani, saida nayi mai isata sannan na fad’a k’irjin nasa ina raira kuka.
Lumshe idanunsa yayi yasaka hannayemsa ya zagayeni sosai yana kuma sakani jikinsa sosai. Nima sainayi luf Ina shak’ar k’amshinsa da yariga ya mannema fatarsa.
Munja wasu times a haka, ni ina kuka shi kuma idonsa a lumshe yana shafa kaina da saurarena.
Jiyay kawai jikinta ya saki, alamar barci ya d’auketa, sai ajiyar zuciya da take ta saukewa, bud’e idonsa yayi, sannan yakai bakinsa a hankali ya sumbaci sumar kanta dake tare da danshin ruwa har yanzu. zafin zazza6inta dake ratsa 6argon jikinsa ya sakashi fidda huci yana kuma sumbatar kanta.
Dr Farida ta sanar masa babu abinda zai hanata wannan zazza6in, koda tasha magani ya sauka saiya dawo, sai idan cikin yayi kwarine maybe ta daina ma gaba d’aya, amma mai juna biyu ba’a rabata da k’ananun ciwo makamantan haka. jiyay ya kuma k’aunar Momma d’insa a ransa, a hankali ya furta I love you my Momma”.
Tashi yay d’auke da Munaya a hannu, ya kwantar da ita sannan yaja bargo ya lullu6a mata. tare da sunkuya wa ya sumbaci goshinta ya shafa cikinta da hannunsa sannan ya mik’e ya koma inda yake.
Ya cigaba da aikin dayake a laptop Wanda ban fahimci komaiba a ciki, tsawon lokacin yana aikin, saida ya fara hamma sannan ya kashe. bayi ya shiga ya d’auro alwala, ya gabatar da nafila kafin yay shafa’i da wutiri yaja doguwar addu’a da kirari wa Ubangijin talikai, harda hawayensa sannan ya mik’e.
Ya kuma daidaita hasken fitilar d’akin sannan ya hau gadon shima ya kwanta, yay musu addu’a ya shafe cikin munaya (??Galadima saboda tsaro ba tsoroba ko??).
a zatona zai rungumeta, sai naga ya gyara kwanciyarsa kawai a gefenta yaja bargo shima.
Galadima asuba ta gari, (ni dai rungume nawa mijin zanyi aradu?????????).

Ga bannin asubahi zazza6in munaya ya sauka, hakanne ya sakata samun dad’in barci sosai, ta kuma kanainaye Galadima, wanda shi da kansa ya mirgino har inda take cikin barci ya rungumeta, dukda zafin zazza6inta nata ratsa nashi jikin yakasa barinta. ahaka kiran sallar farko ya riski kunnuwansu.
Kusan a tare suka farka, ganinsu manne da juna yasaka kowa barin jikin d’an uwansa da sauri, munaya dai kunya ta sakata juya baya, amma boss ko a kwalar rigarsa, saima tashi da yayi yana wani ciccin Magani ya shiga toilet.
Alwala ya yo, baiyi mata magana ba ya fice abinsa.
Munaya ta raka bayansa da harara tana fad’in Girman kai dai rawanin tsiya wlhy. tashi tayi itama ta shiga bayin, amma sa6anin shi ita harda wankan gasa jiki (lallai kinji basawa Munaya??, wannan gasa jiki dabaya k’arewa haka????).
Fitowa tayi tanata kumbura fuska, ni dai na lalla6a na shige bayinta danna dandalo arzik’i?? lol (koya kukace fans?????????).

****************************

Ban sake jin d’uriyarsa ba sai around 9:30am.
Tashina a barci kenan na rarrafa zuwa bayi da k’yar nayo wanka, dan banajin dad’in jikina gaba d’aya, danan ya saki sai nan ya kama ciwo.
Motsin mutum naji a bayana dan haka na waiga, Galadima ne cikin Farin wando da t-shirt itam fara tas, ya d’aure k’ungunsa da Navy blue d’in belt, sannan ya kawo jacket navy blue itama ya saka, babu takalma a k’afarsa, sai dai k’afar fes tamkar ba’a takata a k’asa, sai agogon azurfa mai k’yau d’aure a tsintsiyar hannunsa.
hummm dan k’yau kam dai yayishi, sai dai ni bawai ya birgeni bane?? (ho Munaya banda zuk’i ta malli dai??????????).
Janye idona nayi na maida kan gyaran gashina da nakeyi.
Shima baice uffanba ya wuce wajen frigate, fresh milk ya d’akko yatako gaban mirror inda nake zaune. a saman mirror ya ajiye kwalin madarar ya jingina bayansa shima, idonsa a kan gashina danake gyarawa. ya d’au madarar ya zuba a cup d’in daya d’akko tare da mik’omin.
“ni ba ita zan shaba”. na fad’a ba tare da na kalleshi ba.
“mikenan?”. shima yafad’a cikeda k’asaita.
Yanzunma ban kalleshi ba nace “tea”.
Kofin ya dire saman mirror yana tattare hannun rigarsa, “salon ki k’onamin idon abin cikin kwan kenan, to za6i ya rage naki, sha da arzik’i ko kuma d’ura”.
Babu shiri na d’auki kofin na kwankwad’e, dama iyayine inajin yunwar.
Kofin na mik’a masa ina 6ata fuska tamkar zan fasa ihu.
Ya d’agamin gira yana fad’in “taimakon kai my friend”.
Gefe nayi da fuskata ina fad’in “kai duk salon mugunta ka sani ai”.
“martabar gudan jinina nake karewa”. yay maganar yana k’ok’arin ficewa.
Baki na na ta6e ina harar bayansa, su gudan jini anji jiki kuwa.
Ganin zai fice nai saurin cewa “nifa inason zuwa kitso, kuma zan koma school”..
Tsayawa yay cak daga yunk’urin fitar da yakeyi, Batare daya juyoba yace “babu wannan tsarin a masarautar gagara badau”.
Yana gama fad’a ya ida ficewarsa.
Tamkar zan fasa kuka nayi jifa da cumb d’in hannu na ina fad’in “ina ruwana dawani tsarinku ni, makaranta ta nakeson komawa ehe”.
Yana jiyota amma ko’a jikinsa yaci gaba da k’ok’arin fitarsa hankali kwance.

?????????

Tunda Aryaan ya shigo da gudu inna ta tareshi tana fad’in “kai lafiya? minene na gudu?”.
“innarmu wlhy Uncle ne yace ki shirya mana kayanmu ni da Aiyaan zai aiko gobe a kaimu wajen Auntynmu”.
Inna tayi d’an murmushi kawai, dan ita bata d’auki maganarma serious ba.
Su dai su Aiyaan sunata murnarsu, sun tafi d’aki sun hau had’a kaya.
Babu dad’ewa da yin haka saiga daddy ya shigo da sallama, inna ta amsa masa tana gyara zama, shima zama yay kujerar dake kusada k’ofa, ganin haka inna ta fahimci da magana yazo, dan haka ta maida dukkan hankalinta Kansa.
Bayani yamata dalla-dalla akan zancen da su Galadima sukazo dashi, ya d’ora da fad’in “saiki shirya dan zamuje ai miki passport”.
Inna tace, “amma dadynsu nake ganin ai da kud’in kukaje kamar zaifi”.
Murmushi Dady yayi, yace “Ai’sha nasan miyasa kikeso zamewa, to ai kaf cikin matan yayan kece ya cancanta kije koda ace bawai Galadima ne ya biyaba, maganar ciwo Muke bawai jin dad’i ko gutsiri tsomar wasu ba, ki shirya dan zai turo wanda zamuje immigration office d’in”. daga haka ya tashi ya fice.
Shiru kawai inna tayi, itadai inda ta itace da antafi da ko innaro, dan tasan wannan tafiyar dukda ta ciwoce sai ta janyo 6acin rai a gidan.

Aiko tamkar inna tasani, dan ana fad’ama innaro tace “bata amince ba, ita ta haifi auwalu kuma da ita za’aje tayi jiyyar yaronta, bazata bama kowacce mace acikinsu wannan ragamarba.
Shiru baba k’arami da daddy sukayi, taci masifarta ta gama tayi shiru.
Baba k’arami yace, “amma dai inna kinsan jinyar Yaya sai da matarsa a kusa, kekuma k’arfinki ya k’are ya za’a d’ora miki d’awainiyar da matansa ne keda hakki a kai?”..
“yo d’awainiya ba tare da kai za’a tafiba? Kai basai kamasa ba. ni dai fa ban amince Ai’sha tajeba, dan wlhy bazan ta6a son Ai’sha ba komi zata zama, tunda dai ta silar jikokinane balle amin ilimi. k’ilama itace ta jefeshi dan taga ta kama k’asa ‘yarta Na auren d’an Sarki, t……..”.
“innaaaa! haba mana, dan ALLAH karma ki bari maganar nan ta fita, waishin minene laifin Ai’sha a gareki? duk cikin matanmu banga wadda take girmamaki da d’aukarki matsayin uwaba irinta, inna ya kamata wannan k’iyayyar ta koma soyayya hakanan, a baya kince dan basuda asali, kin dawo kince juya ce bata haihuwa, gashi kuma yanzu har ALLAH zai fidda jikoki daga tsatsonta, to miye kuma matsalar?”.
“toko zaka shak’eni Na fad’a makane Hameesu?”.
“a’a inna, ALLAH yabaki hak’uri”.
“kaidai ka Sani, ni yanzu bara Na tashi Na shirya Ku kaini inama kace, imagesa nema ko uwarmi oho”.
Daga Dady har baba k’arami babu Wanda ya tanka mata, tana shigewa baba k’arami ya mik’e yana cema dady “yaya ka jireta, bara naje mutafi da maman ‘yan biyun, kota fito kace naje shiryawa ne”.
Kai Dady ya kad’a masa yana murmushi, baba k’arami ya fita da hanzari.

Bayan wasu mintuna saiga innaro an fito ana warware gyale za’a yafa, “yauwa jafaru muje Na shirya”.
Habiba dake kitchen tana girki duk diramar da ake tana saurare ta tuntsure da dariya, lallai tsohuwarnan akwai daru, mama Na hanya ai, itace maganinki (gwaggo Safiyya mamarsu).
Kallonta Dady yay yana murmushi, yace “to inna mu jira jafar d’in yaje shiryawa”.
“ato shikenan bara kafin ya dawo nad’anci abinci, k! Habiba zubomin idan abincin nan ya tsotse, gara Na fita cikina da d’an nauyi”.
Habiba ta had’iye dariyarta sannan tace “innaro bai tsotseba, amma nanda kamar dai minti 5”.
“babu damuwa ai, nasan jafaru ma bai dawoba harnaci, kinsan shi da dak’undar shiri, ya tsufa amma kullum kallon kansa yake sa’ar Abdul-hameedu”.
Dariya Dady ya had’iye da k’yar, yasa handkerchief yana toshe baki dan karta fito.

????????

Tsaf na kammala shiryawa sannan Na kimtsa d’akin, ni dukfa a nufina nayi shirin asibitine.
Fitowa nayi dan naga ko yana falone, wayam babu kowa, sai sallama da nakeji a bakin k’ofar, amasawa nayi na bada izinin shigowa saboda naji muryar matane.
Su 10 ciff suka shigo, k’asa suka zube suna gaisheni, Na amsa musu da ‘yar sakewa, “lafiya dai?”.
“lafiya lau ranki ya dad’e, mune zamu kasance hadimanki, masu miki dukkan hidima.
Nifa wlhy banason wasu bayi, amma dolene Na barsu tunda wad’ancanma Galadima ne yace su tafi, yanzu kuma baya wajen, ni kuma banida ikon korarsu tinda bansan kan abinba.
Amsa musu nayi da “to” sannan nawuce Na zauna a kujera.
Tasowa sukai suka biyoni, a tsanake suka dinga fad’amin sunansu da aiyukan da zasuyi.
Wad’anda naga bazan iya yarda suyiba Na canja musu aiki. Sallamarsu nayi, Ina k’ok’arin tashi Na shige ciki saiga Sauban ya shigo, duk zubewa sukayi suna kwasar gaisuwa a gareshi, ya amsa musu yana wani yatsine face, sai kuma ya basu izinin tafiya, fita sukayi harabar sashenmu.
Na kalleshi ina murmushi, “ashe kaima dai sarautar Na jininka yaa Sauban? Wanda bai saniba saiya d’auka duk bazaka iya wani Abu daya shafi sarautaba”.
Dariya yayi yana zama, “aunty gimbiyar mu kenan, wannan ai sai mijinki”.
Nima murmushi nayi kawai.
Ya mik’omin kayan hannunsa yana fad’in “ga break fast d’inki”..
“wayyo yaa Sauban, nikam dai nagaji da ciye-ciyennan ma, zuwa zanyi Na fara abinci da kaina”.
“wlhy dakin taimakemu Aunty gimbiya, mijinki shiya saba da cin abincin waje shiyyasa bai damu ba, ya kamata kafin Na wuce gobe naci girkinki”.
“kamarya gobe? Kana nufin zaka koma kenan?”.
“tab da gudu kuwa, aini bazan iya zaman k’asarnanba Na tsawon lokaci, tarema zamu wuce da Abba ai, harma da innarmu, yaa Sam bai sanar dakeba kenan?”.
Baki bud’e Na girgiza masa kai alamar a’a.
Sauban yay murmushi, “kinsan halin Galadiman namu ai, soyake yamiki surprise maybe, yanzu hakane yaje cuku-cukun visa d’insu ne. waito miyasa bazamu koma tare da kubane?”.
Murmushin yak’e nayi, nace, “maybe akwai ayyukan dabai gamaba shiyyasa”.
“inaga hakanne kam, ni bara naje, yace Na iskeshi birnin gayu, ga mahfuz can Na jirana”.
“ok sai kun dawo” Na iya cewa, danni daga ‘yan matan masarautar har samari ba kowa Na saniba, tunda time d’in daya kamata nad’an San mutane sai muka tafi India. ni bama nason Na saba da kowa, ni da ba zama ya kawoni ba.
Maganar fita da Abba da Galadima yakeyi sai yayta cin zuciyata, kimar Galadima da darajarsa saita cika zuciyata, inason mahaifana, kuma dukkan Wanda zai nuna musu kulawa bazan manta da shiba, harda ‘Yar kwallata Na share, Na tashi Na koma bedroom ba tare da nayi break fast d’inba ma.

*****************************

Innaro dai tun ana jiran dawowar baba k’arami harta fara gyangyad’i, habiba data kammala abincin ta d’ebo ta kawo mata, nuni Dady yay mata akan ta koma.
Habiba ta koma da baya ba tare da ta k’araso falonba.
Tun tana gyangyad’i harta 6ingire a kujerar barci mai nauyi ya d’auketa (ho innaronmu ta mutunci????????).

Baba k’arami da innarsu munaya kam tuni sunyi ficewarsu, dayake Abu Na kud’i dandanan aka gama cuku-cukun komai, Nuren ne tsaye, saida komai ya daidaita suka samu visa d’insu a hannu sannan suka fito.
Har gida ya maidosu ya koma suna jera masa godiya da addu’a shi da Galadima.

Innaro daga gyangyad’in jiran abinci ya tsotse aka zarce da barci mai nauyi, shima Dady lalla6awa yay ya fito dan asibiti zaije.
Tafiyarsa babu dad’ewa saiga gwaggo Safiyya ta iso da yaranta biyu.
Hayaniyar su Dahiru ita ta tada innaro, ta mik’e zumbur tana fad’in “yauwa Jafaru kadawo mu tafi ko? Habiba bar abincin kawai idan muka dawo naci.
Mi Dahiru da Naja’atu zasu ba dariya ba, suka shiga shek’ama innaro dariyar shak’iyanci. Wai kota kwanta da yunwa ne.
Zaginsu ta hau yi ta d’auki filon kujera tana dukansu.
Sai da gwaggo Safiyya ta musu magana sannan suka nutsu, “inna ina zakuje da Jafaru ne?”.
Gyara zama innaro tayi tashiga bama gwaggo Safiyya labari.
Murmushi kawai gwaggo Safiyya tayi, danta gane wayo suka mata suka gudu kawai, itama sai tace “to inna ki cigaba da jiransu, k’ila dan sunga kina barcine suka jira ki tashi sannan Ku tafi.
Da wannan gwaggo Safiyya ta rufe bakin innaro ta zauna jiran su dady.

Aiki??????.

**********

Galadima daya fita kai tsaye asibiti ya nufa, su yaa hameed kawai ya iske can, dan dady ya hana matan gidan zuwa sai anjima, doctors Na complain akan suna cika wajen da yawa.
Cikin mutunta juna Galadima ya gaisa dasu yaa sabi’u sannan yashiga yaga daddy.
Yau kam Alhmdllh dan ba barci yakeba, kumbirin fuskarsa kuma yad’an sa6e kad’an, saidai baya iya magana sai dai yayta bin mutane da idanu.
Dukda bazai iya amsawa ba haka Galadima ya risinna ya gaidashi, tare da masa fatan samun lafiya sannan ya fita office d’in doctor.
Bayan sun gaisa doctor ya bama Galadima file d’in bayanan Abba dasuka tattara.
Kar6a Galadima yayi ya duba, dukda bawai ya fahimci bayanan bane, ( kusan dai rubutun doctors sai su). Suka d’an tattauna akan cigaban da aka samu sannan Galadima ya fito.
Ya iske daddy ya iso, suka gaisa sannan yamasa dukkan bayanan da doctor yamasa shima. Dady ma yaji dad’in cigaban da aka samu.
Galadima yay musu sallama ya fito.

Guntun tsaki yaja saboda yanda jama’a suka wani zuba masa idanu tamkar sunga magiji, da sauri wani dogari ya bud’e masa motar ya shiga, sannan suma suka shiga.
Daga asibiti Galadima yace su wuce birnin gayu plaza.
Cike da girmamawa sarkin mita ya amsa da to.
Maida kansa yayi jikin seat ya kwanta tareda lumshe idanu ya fad’a duniyar tunani…………….???

Barkanku da juma’a??????????.

Musha weekend lafiya sisters??????????????????????.

*_ALLAH ka gafartama iyayen mu_*??????
*_Typing??_*

*_Haske writer’s asso…._*??

*_?RAINA KAMA……?_*
_{Kaga gayya}_

*_Bilyn Abdull Ce_*????

_________________________
_Duk marubucin daya kafa alk’alaminsa bisa takarda tabbas yagama tanadar yanda labarinsa zai kasance ne, amma sai wasu wabubuwan mamaki kaga sun gaza k’arewa a social Media, ban saniba ko samunmu available ne yakesa a kullum kuke mana kallon marasa aikinyi?, ni dai nasan time d’in dana shirya labarin RAINA KAMA ban zauna tebirin shawara da kowaba a online, inkuwa hakane tayaya wasu har suke tunanin nafara sauka akan layin labarin?, to magana d’aya zanyi a wannan ga6ar, ban gina labarin Raina kama akan kwanciyar aure bane, dan haka masu maganar munaya bata da aiki saima Galadima rashin kunya saisu jira saina kai k’arshen labarin kafin su k’alubalanceni, abin dariya, (wai aikina kenan daga nasa munaya ta murgud’a baki sai ta harari Galadima da masa k’unk’uni) tunda aikina kenan babu lallai wajen 6ata lokaci karantawa, haka Na tsara labarina tun farko kuma haka zanyi, duk wanda yaga bai masaba zai fara iya rubuta nashi shima kawai. wannan abun da kukema writer’s yana 6ata mana rai, bai kamata ku dinga k’alubalantar writer’s ba, bayan su suke da masaniyar yanda suka shirya labaransu, idanma zakuyi saiku ringa tanadar lokaci har zuwa bayan mun kammala, hakan zaifi tasiri fiyeda katsalandan a tsakkiyar labaran mu, akoda yaushe kuzama masu kula kafin Ku k’alubalanci mutum??????._
*Ba akan kaina kawai nayi wannan bayaninba, harda sauran writers da yawa da akema makamancin hakan koma fiye da nawa.????*

________________https://2gnblog.blogspot.com/_____________

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply