Hausa Novels Raina Kama Book 1 Hausa Novel

Raina Kama Book 1 Page 23


Raina Kama Book 1 Page 23
Viral

??2?3?

…………..A saman sofa na iskeshi zaune, ya d’ora k’afa d’aya kan d’aya yana waya. Idanu ya d’ago yad’an kalleni ya janye.
kunyace takamani saboda babu ko gyale ajikina, gashi kayan sket da rigane, kamar munafuka haka nawuce inda akwatina yake da aka kawo da safe, nima farkawa nayi kawai na gansa a d’akin.
Gyale na d’auka na yafa, sannan naje bakin gadon na zauna ina sauraren wayar dayakeyi, abinda na fara lura da halayensa shine, shi mutumne marason hayaniya, komai nasa zaka sameshi a nutse yakeyi, yanzu haka a d’aki d’aya muke zaune, amma ba komai nakeji ba a maganar dayakeyi, ga jan aji tamkar wani mace, jinin mulki dake yawo a jikinsa ne ke k’ara masa k’asaita da izza…….
Gyaran muryar da yayce yasakani d’agowa na kalleshi, idonsa a kaina, Dan haka muka had’a idanu, kowa janye nasa yayi cikeda basarwa.
Saina samu kaina da cemasa “ina kwana”.
Saida yaja wasu seconds sannan yace, “kin tashi lafiya?”.
“Alhmdllh” kawai nace masa nayi shiru.
Shiru mukayi babu Wanda yasake magana, yanata aikin latsa wayarsa, nikam ina satar kallonsa da mamakin wannan halayya tashi, shi koma takura bayayi? ina dad’i dan ALLAH kai kenan kullum baki 6am??.
Kusan mintuna 5 muna a haka, bakajin komai a d’akin sai k’arar AC, ni dukma sanyin ya isheni. batareda ya d’agoba yace “mikike buk’ata akawo miki break fast?”.
ALLAH shi k’yauta, nafad’a a raina kafin nace, “ko miyema”.
Idanunsa ya d’ago yana kallona, baice komaiba ya janye ya mada ga wayar. sai kuma yasaka a kunne, “mom ki basu su kawo abincin ta tashi”.
Bansan mitace masaba daga can, naga dai yayi murmushin gefen baki tareda yanke wayar.
Ya kalleni yana gyara zamansa, tareda kuma shan mur alamun maganar da zaiyi important ce, “ki kimtsa su mom zasu iya shigowa a kowanne time, dan zuwa anjima zasu tafi, duk yanda dai zaki nuna musu wani Abu yashiga tsakanina dake kiyi, dan banason su tafi dawani zargi a ransu OK?”.
Duk da na fahimci inda zancensa ya dosa, hakan bai hanani yimasa kallo mamakiba, nace, “kamar ya ban ganeba fa ni”.
Shima kallon mamakin yamin, kamar zaiyi magana saiya fasa kuma, yad’an furzo huci a bakinsa kafin ya cije lips nashi da d’an k’arfi. tsaye yamike yana zuba wayoyinsa cikin aljihun ash d’in wandonsa, sannan yafara tafiya, sai da yakusan fita sannan yace, “ki nuna musu tamkar wata mu’amullar aure tashiga tsakaninmu, wannan shine kawai mafita, idan kin gama kizo kiyi breakfast”. ficewarsa ya ida yi.
Yayinda nikuma na sauke ajiyar zuciya, danni maganganun nasa duk sunzomin a cirkud’e, to mom d’in nasa ba’a gidan takeba kome? Sannan kuma ai mu yakamata muje mu gaisheta bawai ita tazoba aganina, mi hakan ke nufi?. banida mai bani amsata, dan haka namik’e a gadon ina sauke numfashi, inason kiran Munubiya amma ina tsoron yaa marwan. wayar innarmu nakira, amma a kashe, idona yacika da k’walla, murya na rawa nace “wayyo innarmu I miss u wlhy”.
jinake tamkar nayi tsintsuwa naganni a gida, dama ashe akwai randa zatazo na kwana Na tashi ba’a gidanmu tareda munubiya taba? gaskiya masu cewa aure da dad’i basuda kai wlhy, dan ALLAH ina wani dad’i anan?.
Da Sauri Na goge hawayena saboda jin maganar Samha a kaina, jikinta a sanyaye ta zauna kusada ni, nima saina yunk’ura natashi zaune ina murmushi da share sauran hawayen fuskata.
“Samha yaushe kika shigo”.
Kanta ta langa6e gefe cikin damuwa tace, “Aunty yanzu na shigo, miya sakaki kuka? ko Uncle Sam…. ne?”.
Murmushi namata, danni dariya wannan shagwa6ar tata ke bani, ko kad’an bata d’aukar kanta ta girma, “A’a Samha, ba shi baneba, ina kika shigene haka?”.
“ina nan, tun d’azun naso zuwa Amma mummy ta hanani, yanzu ma tare muke dasu mom, suna falo kisaka Al’k’yabba muje”.
Kallon jikina nayi, nace “bara dai na saka hijjab, ALLAH Alk’yabba d’inan nauyi takemin”.
Dariya Samha tayi, “lallai aunty ai Indai kina gidannan dole saikin sakata, sai dai indan kun taho india, yanzu mafa dole ki saka”.
Badan nasoba na d’akko Samha ta tayani sakawa, sannan muka fita bayan nafesa turarrurruka na masu dad’in k’amshi.
A zatona suna falona, ashe suna nashi, Samha na rik’e da hannuna tamkar wata ‘yar jagora har sashensa, Wanda sai yanzune nake d’an kallon wasu abubuwan, dukda face d’ina arufe take da hular alk’yabba. Sallama mukayi a k’ofar falon akabamu izinin shiga, gabana na dukan tara-tara muka shiga, duk zatona irin sunada yawa d’innanne, saina gansu su 5 kawai, kuma duk manyane, mom kawai na gane acikinsu, sauran ban sansuba, saikuma shi boss d’in yana zaune a kujerar mai zaman mutum d’aya kamar ma yana wayane. ban zauna akujera ba sai a k’asa, mom tayi saurin fad’in “a’a d’iyata tashi ki zauna saman kujera mana”. kaina na girgiza muryata a raunane nace “a’a nanma ya isa” sannan a ladabce na gaishesu. cikeda fara’a da sha’awa suka amsa, shi kansa uban gayyar saida ya kalleni, yaji dad’in girmamawar dana bama k’annen mahaifiyarsa.
Samha ta gwargwad’ama mom magana a kunne, wai ta iskeni ina kuka. murmushi kawai mom tayi, tasan kukan bai wuce na shiga kwaryar manyaba, ga d’an nasu dagani jarumine (aikam mom ragone tunda ba abinda kike tunanin bane????).
Kallon Galadima tayi dake harar Samha, “gulmammiya mikike fad’a? tashi kibar falon nan”.
Tashi tayi tana tunzura baki, “wlhy Uncle Sam ni Vance wani abuba, Mom dan ALLAH wani Abu nace?”.
Murmushi mom tayi, tace “a’a bakice komaiba”.
Batareda ya kalleta ba yace, “naji, tunda kin rakosu wuce ki tafi”.
Fita tayi tana daddaga k’afafu, yaja guntun tsuka, yayinda su mom suke mata dariya da tsokana irinta kakanni, nidai kaina na k’asa nima ina murmushin rigimar ‘ya da Uba, duk dama har yanzu bansan yasukeba, naji dai tana Uncle kawai.

Bayan fitar Samha d’aya acikin matan ta kalleni, d’iyarmu cire hular kisha iska kinji, mu nan duk iyayenki ne, daina jin kunyarmu.
Babu yanda na iya, dole na zame hular Alk’yabba d’in, amma kaina na duk’e sosai yanda bazasuga fuskataba, nasiha mai ratsa jiki da 6argo suka Shiga mana daga ni har harshi, duk jikinmu sai yayi sanyi k’alau, nikam kukama nakeyi, Dan dama kad’an nake jira a ta6ani na fashe. sun dad’e sosai sannan suka ajiye min k’yaututtuka suka tafi harda shi domin musu rakkiya.
Bayan fitarsu saina shiga rera sabon kuka, saida nayi mai isata sannan natashi da nufin tafiya nawa d’akin, kallon falon nashiga yi, masha ALLAH, komai yayi a falonnan, kujerun Navy blue ne, sai labuloli da Carpet sun kasance Silver da kwalliyar k’ananun flowers blue, babu wani tarkace sosai, wani hotonsa ne yay masifar d’aukar hankalina, gaskiya hoton ya d’auku, yana sanye cikin kayan sarauta akan dokin dashima yasha kwalliya, murmushin dake d’auke a face nashi shine Yakuma k’awata tsarin hoto, ga hoton irin k’aton nanne kamar kamasa magana ya amsa maka.
Na juya na kalli d’ayan dake bangon kudu, shikam sanye yake cikin farin wando k’al da farar riga itama, ya tsuke k’ugunsa da bak’in belt, takalmansa da hularsa duk bak’ake, yana awani k’aton filine daya k’awatu da korayen ciyayi, hannunsa rik’e da wani k’arfe ga k’aramar boll a gabansa, nan ma fuskarsa washe da murmushi, har hakwaransa sun fito waje, a raina nace dama d’an wasan Golf???? ne? kokuwa yasaka kayanne kawai?.??
Da sauri na juyo jin motsi a bayana, sai kunya ta kamani ganinsa tsaye hard’e da hannayensa a k’irji yana kallona, gudun karya zaci kallon hoton nake sainayi saurin cewa “dama kana buga Golf? ”.
Murmushin gefen baki yayi, yatako a hankali ya zauna a kujerar dake kallon hoton, shima idonsa na kan hoton, ya d’ora k’afarsa d’aya kan d’aya….
Jin yayi shiru yasani juyowa na kalleshi, a tunanina kobai ji baneba, ido muka had’a, kowa ya janye cikeda basarwa, saiya lumshe nasa tareda jingina da kujerar, tamkar anmasa dole yace “kinason wasanne?”.
Nace, “kusan haka, duk da bansan kan wasanba har yanzun”.
Murmushi naga yayi kawai amma baice komaiba.
Nima saiban sake cewa komanba na juya zan fita. idanu ya bud’e yabini da kallo harna fice.
Yana mamakin yanda bata da tsoro, zai iya cewa itace yarinya ta farko budurwa dakan iya masa magana kanta tsaye bada wani shakkuba atare da ita.
Tabbas a wannan fagen ya yaba mata, domin takafa tarihin da manyan ‘yan mata masuji da mulki da Kansu suka kasayi, akwai ‘ya’yan sarakuna da yawa dakesonsa amma sukan kasa fad’a masa, sunsha shan alwashi akansa amma da zarar sun had’u dashi sai alwashin nasu ya gudu, hakama ‘ya’yan manyan attajirai, kuma baisan abinda yasa sukejin shakkar tasaba, shidai kawai abinda yasani baya sakar musu fuska, to ita wannan tatsitsiyar yarinyar koda fuskar tasa takai hadarin gabas murtukewa bata Shankar masa magana, ya cige lips nashi yana ta6e bakinsa wanda shiyasan dalilin yin hakan.

??????

Mama Fulani tagama cika tayi fam da rainin wayon Galadima, ba’a ta6a angon dayay abinda Galadima yayiba a masarautar, duk randa ango zai shiga d’akin amarya za’a kai farin k’yallen dasuke kira (yankin mutuntaka) a shinfid’a agado, washe gari za’a aika a d’ako domin kowa yaga mutuncin da yarinyar takawo, sannan dolene kuma kakawota da safe ta gaida matan Sarki da Sarki kafin yafita fada, saikuma sauran jama’ar gida wad’anda suka kasance iyaye.
Amma saboda rashin mutuncin fand’ararren yaron can anje d’aukar k’yallen yace zai kawo da Kansu saboda shine shugaban marasa kunya na duniya, ta aika bayi masu hidima damata CID ya korosu wai zai nemesu, gashi ana neman k’arfe uku na yamma amma har yanzu baizo gaisuwa ba shida matarsa, sai bayintane ke sanar mata sunga yarako dangin uwarsa lokacin dazasu tafi, amma ita tunda yazi bikinnan bama ta sakashi a idonta ba sai ranar da akayi Mother’s and tarbar amarya event ta gansa awajen. yaron nanfa yana shigar mata hanci da yawa fa, bari taga iya gudun ruwansa da k’arshen wutsiyar iskancinsa, ai ko ubansa bai Isa mata abinda gagararren yaronnan ke mata ba a gidannan.

???

Shi baima San tanayiba, Dan tun bayan fitar Munaya daga sashensa yatashi zuwa masallaci sallar azhur, ana idarwa ko yarda su had’u da Sarki baiyiba ya shiga gida, shigewarsa yay bedroom, yayi kwanciyarsa domin yasamu yad’an huta, jikinsa duk ciwo yake masa, saboda ainan-ainan na al’adar biki, dukda yasan ko Rabin hidimar da harun yayi shi baiyiba, saima ka rantse Harun shine angon wlhy.
Bai wani dad’e da kwanciyar ba barci ya kwasheshi hankalinsa kwance.

????

A gidanmu ma dai bak’i kowa yakama gabansa, an barsu daga su sai su, da daddare Abba yace ashirya da safe kowacce abita da akwatunanta, shi baiga dalilin ajiya ba.
Duk sun amsa da to, amma kowacce burinta ace da ita aka kai nawa, Dan sunason suyo kallon kwaf, basu gamsu da labarin da ‘yan kai amarya suka fad’aba akan gidana Dana munubiya, su a tunaninsu ma an aurenine domin a maisheni baiwa, yaushe nakai matsayin da har d’an Sarki guda mai sarautar Galadima zai gani yace yanaso, bayan lungu da sak’on hotunan mun gama zagaye duniya ni da shi.
K’ilama da gaske yagama lalatani d’in.
Haka dai sukaita gutsiri tsomarsu da kushe irinta masu hassada, duk da wasu abubuwan suna dawo kunnen innarmu batako damuba, ita dai babu abinda zatace ma ALLAH sai godiya, tunda ‘ya’yanta kowanne yasamu matsugunni, yanzu saita maida hankalinta ga ibadar ALLAH da tarbiyar yaranta biyu maza dasuka rage, sune basu gajiba indai tozarcine.

?????

Zuwa la’asar mama Fulani tafara k’ananun magana akan rashin nuna shaidar Munaya takawo budurcinta, dakuma rashin fitowarsu gaida mutane.
ALLAH Sarki Aunty Mimi sai abin ya dameta ganin yanda aketa k’ananun magana a masarautar, hakkane yasata nufar sashen Galadima, babu zancen jiran a mata iso, sarkin k’ofa yabata hanyar tashiga.
Tun’a falon farko daya raba sashina da nasa tace bayinta su jirata.
Babu kowa a falonsa, Dan haka ta zauna tad’au waya ta kirasa, dan batasan halin dayake acikiba, baikuma kamata tashiga kai tsayeba, balle yanzu yanada mata.
Fitowarsa kenan daga wanka saboda tashin dayayi a makare baisamu sallar la’asar ba, sai anan d’aki yayita sannan yashiga wanka. Wayar ya kalla yayinda yake goge ruwan fuskarsa, ganin aunty Mimi yasashi picking call d’in, saiya saka a Hans free yana cigaba da hidimarsa.
“my aunty kin 6uya fa”.
“na 6uya ko ka 6uya my k’ani, gani zaune ai a falonka”.
“kai haba dai? to bani kamar 5minutes na shirya nafito”.
“ok babu damuwa”.
https://2gnblog.blogspot.com/
Bai wani dad’eba yafito sanye cikin farin boyal mai shara-shara, yayi k’au sosai, sai zabga k’amshin turarensa yakeyi na koyaushe. daga shi har Aunty Mimi suka sakarma juna murmushi, ya zauna kujerar dake kallonta yana fad’in “sweet aunty na ni kad’ai”.
“anya kuwa yanzu bamu raba da Munaya ba my k’ani?”.
Murmushi yayi wadda har hak’waransa na bayyana, ya d’ora k’afafunsa d’aya kan d’aya yana gyara zama, “in haka kikeso my Aunty saiku raba ai”.
dariya tayi tace, “nama bar mata. wai kasan mike faruwa a gidannan kuwa?”.
“A’a saikin fad’a”.
“tun kafin tafiyar su mom aka fara k’ananun magana a masarautar nan, wai anzo kar6ar yankin mutuntaka ka hana”.
“mtsoww!” yaja tsaki yana jingina da kujerar da lumshe idanunsa, “Aunty Mimi dan ALLAH karki biyema wannan jahilcin kema” yabud’e idonsa akanta, ransa a d’an 6ace yacigaba da fad’in “kawai da Wanda yakai sanin sirrinka da Wanda ma baikaiba wai duk sai sun sani?, a wace ayar alkur’ani ko hadisi akace dan ka tare da matarka a daren farko sai duniya ta sani?. ita mai aiko a d’auki k’yallen ince agaban kowa na gidannan lokacin da abunnan yafaru take fad’in bakinta bazai iya maimaita k’azantar danayiba?, to kuma tunda tariga da tasan nayi k’azantar abaya miye na aiko da wani k’yallen banza da wofi? wlhy fa suka kaini k’arshe zan shuka rashin mutunci kinji na rantse”.
Shiru Aunty Mimi tayi tana kallonsa, tasan ransa yakai k’ololuwar 6aci, dan Galadima yanada hak’uri sosai, gudun kar matsala ta biyo saboda ciwonsa saita kwantar da murya, “haba my k’ani kwantar da hankalinka mana, ai abun bana 6acin rai baneba kaji, haba my habibi”.
“Aunty Mimi nagaji ne wlhy, rashin mutuncin masarautar nan yafara isata, nifa komai zan iya kawoshi karshe a wannan karon”.
Tasowa tayi ta zauna kujerar gefensa, ta kama hannunsa “please cool down mana my man, kaci gaba da hak’uri tamkar yanda kakeyi abaya, ALLAH yana tare da masu hak’uri, Momma bazataji dad’in wani Abu yabiyo bayaba, hakama Abie duk da yana a kwance zuciyarsa zatayi kunci, kansu ai sukema wa, yanzu ina k’yallen? ”.
Iska ya furzar daga bakinsa, sannan ya nuna mata bedroom d’insa da hannu.
Tashi tayi tashiga, a saman sofa taga k’yallen dan haka ta d’akko ta fito. zama takuma yi a kusa da shi, “my K’ani ina zamu samu syringe?”.
Idonsa yabud’e ya kalleta, “syringe kuma? mizakiyi dashi?”.
“Sameer duk abinda zamuyi mu kare mutuncin mahaifanmu da lafiyarka muyishi mu zauna lafiya. yanzu dai kasa wani ya kawo mana”.
Baice komaiba yajawo wayarsa yakira Muftahu, buk’atarsa ya fad’a masa sannan ya yanke wayar batareda yajira cewar Muftahun ba.
Wata hirar Aunty Mimi ta d’akko masa, tun yana basar da ita, har ya fara tanka ta, daga nan suka cigaba da hira.
Knocking d’in k’ofar akayi, Galadima yace, “waye”.
Sarkin k’ofa yace, “ranka ya dad’e yalla6ai Muftahu ne yazo yace amasa iso”.
“kace ya shigo”.

Da sallama Muftahu ya shigo, ya rissina ya gaida Aunty Mimi sannan yabama Galadima hannu suka gaisa cikin musabaha.
Ledar hannunsa ya mik’ama Galadima, “no kabama aunty mimi”.
Aunty Mimi ta kar6a ta fiddo da Syringe ta 6are daga ledar, had’awa tayi tare da Allurar sannan ta janyo charger ta d’aure tsintsiyar hannunta, Galadima da Muftahu dai kallonta sukeyi, allurar zata tsira Galadima ya rik’e “mizakiyi hakane Aunty Mimi?”.
“Sameer! wannan itace kawai mafita, kabari kawai na d’iba a saka musu, da safe saika basu”.
lips d’insa ya cije da k’arfi, yashiga kwance charger data d’aure hannunta, “ki barsa zan saka musu nawa, yanzu ma koda an saka zai bushene, dan yayi wuri ai”.
“karfa kazo ka shukani”.
“karki damu zanyi, kema kin sani ai, tunda na amsa to zanyin”.
Mik’ewa tayi tana fad’in “shikenan to, bara na duba k’anwata itama”.
Kansa kawai ya jinjina mata, yayinda muftahu yamata sallama ta fice.

“wai mike faruwa? ranka ya dad’e”.
Tsaki Galadima yaja, yay shiru kusan minti 2, har Muftahu ya yanke tsammani da samun amsa. labarin komai yabashi.
Shima Muftahu tsuka yaja, “wai dan ALLAH yaushe za’a daina jahillar al’adarnan a masarautar nan? abinda ba addini ya wajabtaba sun kama sun rik’e, kuma duk matsalar tsohuwar nan ce wlhy, masarautu nawa ne suka daina wannan abun, amma mu takafa ta tsare, ALLAH lokacin da akayi na Uncle Hayatudden, kunya abinnan yabani saboda shi kawai nata6a gani, sashe-sashefa haka akaita nuniyar abinnan a masarautar nan wlhy”.
Wani mugun tsuka Galadima yaja saboda haushi da abin yakuma bashi, fitarma da yay niya saiyaji yafasa.

???

Ni bansan mike faruwa ba ma, ina d’aki kwance duk kewa da kad’aici sun gallabeni, ga wayata babu caji saboda na manto cajan a gida.
Nayi zurfi a tunani naji ana sallama. firgigit nayi sannan na amsa, hijjab d’ina najawo na saka, ina k’ok’arin tashi tashigo. da Sauri na mik’e ina mata sannu da zuwa, dan nariga da na shaidata itace aunty Mimi. rissinawa nayi na gaidata, ta amsa cikeda fara’a sannan ta zauna. mik’ewa nayi na nufi freight domin bata ruwan amma saita dakatar dani ta hanyar kamo hannuna.
“no k’anwata barshi kinji, yi zaman ki, ya zaman kad’aici da bak’unta?”.
Kaina a k’asa nayi murmushi kawai, sannan nace “Alhmdllh aunty”.
“masha ALLAHU k’anwata, babu dai wata matsala ko?”.
Kai na na d’aga mata alamar babu, daga nan mukayi shiru saboda rashin sabo.
Zuwa can nace, “ina Samha?, tun d’azu tace zata dawo amma har yanzu?”.
Murmushi tayi, tace, “sun fitane itada Sauban tun d’azun, amma nasan suna hanyar dawowa kam”.
“Ayya ALLAH ya dawo dasu lafiya”.
Ta amsa da amin tana mik’ewa. har falona namata rakiya, inajin dad’in yanda take nuna tana sona.

*******

A can kuwa bayan Muftahu yafito daga wajen Galadima sai yayi murmushi, tabbas yasamu hanyar dazata zame masa tsanin *CIKAR BURINSA*, da wannan kawai zai iya cin galaba akan Galadima.
Da wannan tunanin ya hau mota yabar masarautar gaba d’aya.

Mikake k’ullawa ne Muftahu???

??????

Bayan sallar isha’i ina zaune ina karatun Alkur’ani Galadima ya shigo, ban daina ba saida na kai aya sannan, na d’ago domin gaidashi sainaga idonsa a kai na.
Janyewa nayi nace “barka da dare”.
Bai amsaba cewa kawai yayi “tashi ki shirya zamuje gaisuwa cikin gida”.
Nima sai ban amsa shiba namik’e kawai na maida Alkur’anin inda na gansa. tashi yayi yafita danya bani damar shiryawa. banja wani lokacin mai tsayiba nafito cikin Alk’yabba, tsaye na iskeshi a falona, batareda yace uffanba yafara k’ok’arin fita, nima sai nabi bayansa batareda na tanka d’inba……………..???

??mun tafi sashen mama Fulani, maison jin yanda zata kaya saiya biyoni.
???????????????

Barka da juma’a??????

*_YA ALLAHA KA GAFARTAMA IYAYENMU_*??????
*_Typing??_*

*_HASKE WRITERS ASSO…??_*
_(Home of expert and perfect writer’s)_

*_?RAINA KAMA……!!?_*
_{Kaga gayya}_

*_Bilyn Abdull ce????_*

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply