Hausa Novels Raina Kama Book 1 Hausa Novel

Raina Kama Book 1 Page 22


Raina Kama Book 1 Page 22
Viral

?2?2?

……….Takun takalminsa yana bada sautine dai-dai da kowacce dak’ik’a na bugawar zuciyata, gaba d’aya saina nemi jarumtata na rasa, musamman da firarsu a Ayusher tashiga dawomin a zuciya.
Zuciyata tashiga tsitstsinkewa, saikace ba Munaya mai tsiwarnan ba da rashin barin kota kwana, kululu cikina yabada sauti lokacin da aka murd’a handle d’in k’ofar. kamshinsa ne ya buso min har cikin hancina.
Shikam cak yatsaya yana kallona da mamaki, yasan wannan aikin aunty Mimi ne ko mom, yakuma tamke face saboda tsaro ba tsoroba??.
Oho ni bamma san yanayiba, nima tawa ta isheni a zuciya, dan wani tsoronsa ALLAH ya dasamin lokaci d’aya. kusan mintuna 2 yana a tsaye tamkar bak’on falon, yayinda k’amshin turarena ke dukan hancinsa, yau da ace auren soyayya yayi da wadda yakeso, babu abinda zai hanasa sauke nauyin daya damesa tsawon shekaru. a hankali yacigaba da takowa har cikin falon, ya zauna a kujera mai zaman mutum biyu cikeda izza, k’afarsa d’aya a kan d’aya yana wani kallona a k’asan idanu, shiru kakeji tamkar bama a cikin falon…….
Muryata a sanyaye nace “ina yini”.
tamkar bazai amsaba, saikuma yace “lafiya”.
Daga nan kowa yay shiru.
Knocking d’in k’ofar da akayine yasakashi sauke 6oyayyar ajiyar zuciya, cikin muryarsa mai kama da anmasa dole ya tambayi wanene?.
Cikeda girmamawa sarkin k’ofar yace, “nime ranka ya dad’e, dama an kawo sak’one”.
Kansa ya jingina da kujera, sannan yace “su shigo”.
Kuyangi kusan biyarne suka shiga falon da sallama, duk muka amsa akan la66a, suka dire kayan hannunsu sannan suka zube suna kwasar gaisuwa agaremu, hannu kawai ya d’aga musu, nidai koma motsi banyiba, dan nima kunyama nakeji idan naga sun durk’usa suna gaidani, danfa wasuma sun girmeni sosai wlhy, wasuma sun haifeni, kai sarauta dabance gaskiya, al’amuransu sunada wahalar gaske, nidai harma yanzu ban fahim ci komaiba wlhy.
Bayan fitarsu da kusan mintuna 4 naji alamar mik’ewarsa, yanzu ma baice dani uffan ba yashige wani d’aki danake k’yautata zaton bedroom d’in sane a wajen.
Guntun tsaki naja, a raina nace ALLAH ka rabamu da girman kai dai wlhy.
Ban damu da cire hular alk’yabba d’inba, dan sanyin Ac yasa ban takura ba, sai zamana dana gyara sosai yanda zanji dad’i da k’yau a saman lallausar kujerar, duk da har yanzun a tsoracen nake kuwa. dan wannan d’an jinkan yafi k’arfina, zai iya amfani da k’arfinsa ya cutamin batareda yayi la’akari da matsayin auren namuba.

Shikam yana shiga d’akin nasa yafara k’ok’arin cire bottom d’in rigarsa, idon sane ya sauka akan gadonsa dake lailaye da zanin gado blue, dan komai nasa na nan white and blue ne, sa6anin na India dasuke White and Golden, kuma matsawa yayi sosai saboda ganin farin k’yalle dake saman bedsheets d’in.
Tsaki yaja yana fad’in “waisu wad’annan mi suke nufi da shinfid’amin wannan farin abun a saman gado? samazo su d’auki kayansu yanda suka ajiye, motsww”. Yakuma jan tsaki sannan ya shige bathroom.
Acanma yana wankan yana jera tagwayen tsoki, bai wani dad’eba yafito sanye da bathrobe milk, hannunsa rik’eda k’aramin towel yana goge fuskarsa zuwa kansa.
Bai shafa maiba, wando yasaka da t-shirt duk milk color marasa nauyi, da alama yayi shirin barci kenan, ya d’auki turarensa na barci mai sanyin k’amshin ya faffeshe jikinsa, sannan ya saka silifas bak’ak’e a k’afarsa yakuma fitowa..
Kallona yayi da mamaki ganin ko fuskarta na kasa bud’ewa, ya ta6e baki da cije lips nashi saman ya zauna bisa tattausan carpet d’in tsakkiyar falon inda kuyangin suka ajiye kayan d’azun.
Tankwashe kafafunsa yayi yashiga bud’e kwanikan domin duba abinda ke ciki. “halan kekam bak’ya jin zafi?”.
Yayi maganar yana zuba fruits salad a k’aramin bowl na tangaran mai k’yau.
Shiru nayi tamkar ban jishiba, shima saiya shareni yaja bowl d’in gabansa yafara sha a hankali tamkar bayaso.
Duk abinda yakeyi ina kallonsa ta k’asan ido, saboda kaina Dana jingina da kujera.
Kusan mintuna 5 yana shan fruits salad d’in tamkar wani k’aramin yaro, dan ko Rabin Wanda yazuba baiyiba, araina nace abincinma sai an masa sarauta kenan.
Idanunsa ya d’ago yana kallona, “k wai bakijin ana Miki maganane? bazaki bud’e face nakiba?”.
Saida naja kusan seconds 20 sannan na janye hular alk’yabba d’in.
Janye idonsa yayi yacigaba da shan kayansa, nikuwa saima na zame na kwanta a kujera, dama 3setter ce, idanuna na maida na lumshe saboda ciwon da kaina yakeyi kad’an-kad’an, ga kewar innarmu da munubiya dasu Aryaan na damuna, ga wannan auren na fargaba na addabar zuciyata.

Dukda yaga kwanciyar danayi bai tankaba, ya kammala shan fruits salad d’in yamik’e, saman kujera yakoma ya zauna, ya d’auki wayarsa yana latsawa, saikuma ya ajiye ya d’auki remote ya canja tasha zuwa labarai.
Haka muka zauna tamkar kurame, shi yana kallon labarai yayinda nikuma barci 6arawo ya saceni batareda na shirya ba, to gajiya na nuk’urk’usata.
Shi duk bai farga barci nakeba harya kammala kallon labaransa ya kashe tvn, kallona yayi da nufin min magana saiyaga kamarma nayi barci a haka.
Yay d’an jim yana tunanin tayaya zai tasheni, danshi soyake ya shige yayi shafa’i da wutiri ya kwanta, a ganinsa kuma bai kamata ya barni a wajenba.
Matsowa yayi kusada kujerar, ya d’an bubbuga hannun kujerar, dama barcin nawa baiyi nisaba, na bud’e idanuna dasukayi d’an jaa a hankali, saboda barcin dana fara.
“tashi muje ki kwanta”.
Gabana ya fad’i, amma saina yunk’ura da k’yar natashi zaune.
Ganin ya nufi k’ofar futa sainaji d’an sanyi, tashi nayi nabi bayansa muka fita, bakowa falon alamun duk suntafi makwanci. Wani falon muka shiga daban kuma, gaskiya shima ya had’u, komai na cikinsa lemon green ne da milk, sai tashin k’amshin turaren wuta da air fresheners masu dad’i yake. bai tsaya ananba yay gaba, nidai ina binsa abaya kawai, munshiga k’aton bedroom tamkar nasa, saidaifa aganina nasan yafi had’uwa duk da ban ganiba, nanma komai lemon green ne acikinsa, sai labuloli milk kamar falon, shima yanata tashin k’amshin.
Juyowa yayi ya kalleni “nan shine d’akinki”. ‘yayi maganar tamkar an masa tilas’.
Uffan bance masaba, sai d’aga masa kai nayi alamar naji, shima bai sake cewa komaiba ya fice abinsa.
d’akin na shiga bi da kallo, yamin k’yau sosai, na cire alk’yabba jikina ina sauke numfashi, sanan na cire sark’a da ‘yankunne da bangles d’in duk na zube saman madubi. Suma kayan na hau cirewa dan bazan iya barci da suba, sai kuma na shiga tunanin inda zan samu kayan barci? tunda lefena suna gidanmu ba’a kawoba, akwatin da’a kawoni dashi kuma jiya ban Ganshi a d’akinba, zuciyatace tabani shawarar duba wardrobe d’in dake d’akin, banyi musuba naje na bud’e, a mamakina saina ganta da kaya, sai dai duk k’ananune, kayan barcinma babu na mutunci, tamkar zan fasa kuka haka naji, da k’yar nasamu wasu Riga da wando masu sauk’in fidda tsiraici, duk da suma d’in dai sai a slow.
Gadon na hau amma saina kasa barci, kewar ‘Yar uwata yadawomin sabuwa, na tashi zaune na fashe da kuka.
Ina zaune ina kukana sai kawai naga mutum yashigo min da sallama ciki-ciki.
Da Sauri na jawo gyalen dana ajiye gefe na yafama jikina, plate d’in hannunsa ya ajiye a table d’in dake jikin gadon, dan harya kwanta yatuna banci komaiba, gani yayi bai dace ya barni da yunwa ba, danni bak’uwace yanzu a gidan, dole sai an bani zanci.
Tamkar bazai tankaba saikuma ya kalleni, “mike faruwa kike kuka?”.
Wasu kwallanne masu zafi suka sake kwararomin, na sharesu da gefen gyalena nace, “wlhy ni tsoro nakeji, ban ta6a kwana ni kad’aiba, dan ALLAH ka kiramin Samha ta tayani”.
Shiru yay ya tsaya kawai yana kallona, azuciyarsa yace kajifa wannan yarinyar dawani batu, kawai saina tafi kiran Samha ta tayata kwana?. guntun tsoki yaja, Wanda yasakani d’agowa na kallesa. Ya cije lips d’insa sannan ya juyo yakuma kallona “mikike nufi da bazaki iya kwana ke kad’aiba? kin san dai babu wanda yasan manufar aurenmu, daga ni sai ke sai muftahu, dolene ki koya ma kanki iya kwana ke kad’ai d’in, sannan inason kisanfa dolene ki dinga canja behavior naki agaban mutane, domin su agaresu aurene mukayi kamar kowa, sannan ta wannan hanyarne kawai zamu iya samun wani avoidance a kan case d’inan, nasan kinada wayo dan haka saiki bud’e idanunki dan kema zaki iya zama security d’in kanki da kanki, game da zaman gidannan kam za’a samu mai koyar dake komai, dan komai a tsare yake, sauran bayani zamuyishi daga baya, kisa a ranki zaman da zamuyi dake zamane na taimakon juna irinna abota, bayan aiki ya kammala zan baki sakinki kamar yanda nayi alk’awari”.
Duk da hawayen dake neman zubo mini haka na had’iyesu, cikin aro jarumta nace, “insha ALLAH komai zai tafi yanda yakamata, kuma zaka sameni mai tsare gaskiya da amana, ALLAH yabamu nasara, ina fata da lokaci yacika komai ya bayyana zaka cika alk’awarin sakina?”.
Batare da ya kalleniba yace, “zaki sameni mai cike alk’awari insha ALLAH koda ace bamu cika shekararba komai ya bayyana zan sakeki, idan kuma ashekara 1 bamu samu yanda Muke soba zamuyi 2 ne kamar yanda nafad’a miki tun farko, amma inama addu’ar kafin shekara komai yazama done OK?, ga abinci nan kici, kiyi addu’a ki kwanta, zakiyi barci insha ALLAH”.
Batareda ya jira cewata ba yay ficewarsa, kusan mintuna biyu idona na kallon k’ofar, saikace zanga dawowarsane, mamaki yabani sosai, dama yana magana mai yawa irin haka? Kuma cikin kwantar da murya. na sauke ajiyar zuciya tareda bud’e plate d’in daya ajiye, gasashen namane mai rai da lafiya, yawu nane ya tsinke, gashi dama inajin yunwa, na mik’e na bud’e fright d’in dana gani ad’akin, ruwane kawai aciki aka zuba, guda d’aya na d’auka na dawo saman gadon na zauna, inacin naman ina hawaye, gaba d’aya kewar ‘yan uwana ta gallabeni, musamman Munubiya, waya na d’auka na kuma gwada kiranta, amma still akashe, wasu hawaye masu zafi suka kuma kwararowa a kumatuna, naman na ture gefe naciga da kukana, saida nayi mai isata sannan natashi nashiga toilet d’in d’akin na wanko fuskata da bakina na d’auro alwala, a fright d’in na saka naman da sauran ruwan na kwanta kamar yanda yabani shawara, addu’ar barci nayi sannan narufe ido. tunani yace salamu alaikum, haka naita juye-juye a gadon, barci 6arawo bai saceni ba sai around 3. daga nan ban sake sanin inda nakeba saida naji ana bubbuga gefen filon danake kwance.
Da k’yar na bud’e idanuna dasuka kumbura saboda kuka da rashin isashen barci. Galadima ne tsaye a kaina, sanye cikin jallabiya ruwan hanta, tamasa k’yau dukda kallon fisha na masa.
Agogon d’akin ya kalla sannan ya juya zai fita yana fad’in “kitashi kiyi salla”.
Da k’yar na iya sauka, dan jikina duk ciwo yakemin, ga barci danake masifar ji. daurewa nayi nafara wanka da ruwa mai d’an zafi sannan nayo alwala nafito, salla na gabatar ta asuba nayi addu’oina sannan namik’e na koma gadon, dan danan barci ya kuma kwasheni.

???????

A gidanmu bayan kwashemu dukkan amare washe gari ‘yan biki suka fara kama gabansu, sai makusanta ne kawai aka bari.
Lokacin da su Ayusher suka koma sun iske innaro na zuba tijara a tsakar gida, wai an munafunceta ba ace ta fitoba lokacin da akazo d’aukata, dama tasan innarmu bak’in ciki take mata karta dangwali arzik’i, to kuwa ita k’adangaren bakin tuluce, babu yanda aka iya da ita, duk wani makirci da innarmu zata shirya mana akan karmu taimaka mata dolene tanan matsayin uwar ubanmu.
‘Yan gidanmu fa abin nema yasamu, saifa aka hau dariyar gatsa-gatsa suda sauran bak’in su.
Innarmu kam murmushi kawai tayi, zuwa yanzun ita ta wuce k’aramar yarinya, dama sarai tasan bawai nadamar gaskiya innaro tayiba, kawai dai wani abu dake a ranta kawai. Ko lek’owa batayi tsakar gidanba, barema tanuna tasan da ita takeyi.
Shigowar su Ayusher da kaya nik’i-nik’i na biki da mom tabasu yasa innaro waryar leda d’aya tana fad’in munafukai, Ashe kune aka tura domin Ku tattaro komai, to ALLAH ya fiku, kafin mai biri yaga mai gona mai gona yaga biri”.
Ayusher zatayi magana mama Rabi’a ta hanata, haka suka shige da sauran kayan suna k’unk’uni.
Innaro na bud’ewa taga duk drinks ne aciki saita biyo bayansu, ledar ta dangwarar a k’ofar falon tana kunfar baki, “bazansha kayan ruwan ba kayan fitsari, yanzu-yanzu a canjamin kokuma na kwashe komai babu yanda za ayi dani dangin tsiya dangin rashin asali, kai ALLAH yarabamu da bak’ar zuciya mai cike da nunkufurci dai wlhy”.
Babu wanda ya tanka mata, Mama Rabi’a ta bud’e komai ta d’iba mata, tanuna ledar datafi kowacce girma da mama Rabi’a bata bud’eba, “to uwar iya, ita waccan ledar miye aciki?”.
Da sauri Bilkeesu ta d’auke tana murgud’a baki, “wlhy babu mai baki wannan, domin a lissafe suke, kuma mu aka bamawa bawaniba, zannuwane”.
“to ‘Yar karoro, kekuma asuwa gand’oki muje biki? Aiba uban wani ya Haifa min Auwalun ba daya haifi munaya, saiki bari sai ALLAH yabaki farin jinin auren koda kansilan anguwarkune sannan kimana iyayi, kujimin bak’ar banza kawai”.
Baki Bilkeesu ta ta6e, suka ja ledar itada feena suka shige tsohon d’akinmu, yayinda su Ayusher da Ameera suka take musu baya.
Daga mama Rabi’a har innarmu babu wanda ya dakatar dasu.
Aiko sai innaro ta saka kuka wai su Ayusher sun zageta agaban innarmu batace komaiba.
Duk abinda ke faruwa ‘yan gidanmu na tsaye cirko-cirko suna dariya.
Yaa Hameed daya shigo gidanne yazo har inda innaro ke tsaye a k’ofar fallon innarmu yana tambayarta lafiya?.
Cikin kuka da shar6e majina ta kora masa bayani, Kansa kawai ya girgiza, danshi lamarin innaro baya burgesa. Da lallashinsa tahak’ura tafita yarakata har gidanta da ledar da mama Rabi’a ta zuba mata kayan bikin.
Acanma zage-zage taitayi tana aibanta innarmu, kunya dukta ishi gwaggo Safiyya ga sauran ‘yan biki suna saurarenta, gwaggo Safiyya fitowa tayi ta baro gidan, gidanmu tashigo tazo tana bama innarmu hak’uri.
Murmushi innarmu tayi, tace, “wlhy babu komai gwaggonsu, ai inna nima mahaifiya tace, mizaisa dantamin Abu yazama ya 6atamin rai, ai ta Isa danine shiyyasa”.
Innarmu ta bama gwaggo Safiyya tausayi, tana k’ara jinjina hak’urin innarmu a ranta, tabbas da acikin sauran matan gidanne da innaro ta magantu, dan ba raga mata zasuyiba, danma suna Shankar mazajen gidan su Abbanmu.

????**•°•°•°•**????

Su Munubiya amaryar yaa marwan, ??baiwar ALLAH taban tausayi, dan kallo d’aya namata nasan yaa Marwan ya ajiye muskilamci ya kashe arna??.
Duk takuma zama wata silent, tana kwance a falonta dayayi k’yau da tsari, hannunta dafe da kanta, idonta arufe tamkar nai barci, tunanin innarsu da kewar ‘Yar uwarta ya gallabeta, gashi tun shekaran jiya yaa Marwan ya kar6e phone nata ya kashe, tayi rok’on duniya yabata takira Munaya da innarsu amma k’ememe ya hana, yadai kira mata innar sun gaisa jiya da daddare, amma munaya yace ba yanzun ba. hawayene suka ziraro ta gefen idonta.
Tun d’azun yashigo yake kanta tsaye bata saniba, tsigunnawa yayi saitin fuskarta yafara share mata hawayen, da sauri ta bud’e idonta, ganinsa yasata tashi zaune tana k’ak’aro murmushi damasa sannu da zuwa.
Bai amsaba, sai zama dayayi kusada ita yajawota jikinsa ya rungume, “haba my baby yanzu kukannan bazai k’areba? ko har yanzu wajen yana ciwonne nasake had’a miki ruwan zafin ki shiga?”.
Kanta ta girgiza masa tana kuma matso hawaye, murya na rawa tace “ina kewar Munaya”.
Tausayi ta bashi, tareda mamakin tsantsar k’aunar da sukema juna itada ‘Yar uwar tagwaicinta, shikuma wlhy bayason kiran Munayar ne saboda karsu shiga hak’in Galadima, amma yanzu kam bashida mafita, yakai dubansa ga agogon falon, 11:49am, maybe zuwa yanzu sun tashi, wayarsa ya d’auka ya lalubo number Munaya yafara kira. cikin sa’a kuwa sai gata tashiga.
Mik’ama Munubiya yayi, cike da d’oki ta kar6a tana murmushi tana hawaye, shi saima abin yaso bashi dariya.

Ina cikin barci naji ringin d’in wayata, da k’yar na lalubota batareda na dubaba nayi picking kawai, a kunne na kara cikin muryar barci nayi sallama.
Daga can Munubiya ta amsa mani.
Ai zumbur namik’e zaune danjin muryar gudan jinina, “Sweetheart kece? Wlhy I Miss u so much ”. ‘nafad’a ina share hawayen dasuka ziraromin’.
Itama Munubiya hawayen takeyi, muryarta na zuga tace “miss u 2 sweetheart, I love you I love you for ever”. sai kawai ta rushe da kuka tareda fad’awa jikin yaa Marwan dake kallonta tana rera kukanta.
Hannu yasaka yana bubbuga bayanta yana murmushi, yayinda nima naketa maimaita mata kalmar I love you ina kuka.
Wayar yaa marwan ya kar6a, muryarsa kawai naji yana fad’in “to kukan ya Isa haka kema, kar Galadima yagani ya d’auka munyi miki wani abune, sai anjima idan kin nutsu masake kiranki”.
d’if ya yanke, batareda yajira amsa taba.
Sai kawai nakuma ruahewa da kuka na fad’a saman filoluwan da suke zube a saman gadon.

Galadima dake tsaye bakin k’ofar yazo dubani saboda dangin mom da zasuzo mana sallama, saiya koma da baya bai bari na gansaba, zuciyarsa tana masa tunanin dawa nake waya? har nake jera masa kalaman I love u?.
Ya d’an ta6e bakinsa, tareda kauda tunanin a zuciyarsa, to shi inama ruwansa, kwana nawane zai bani takardata na kama gabana.
Falonsa yakoma ya zauna yana jan tsakin Aiken mama Fulani na d’azun data tuna.
Yakuma jan tsakin yana gyara zamansa, dolene ya takama tsohuwarnan birki da wuri, inba hakaba tana neman Shiga masa hanci.

Abinda yafaru d’azunne da safe kusan around 7:30, yadawo daga masallaci bayan yaje ya tadani yadawo d’akinsa, zaune yake a doguwar kujera a falonsa yana azkar kamar yanda yasaba a kowacce Safiya ta duniya. sarkin k’ofane yamasa knocking.
“waye?” yayi tambayar batareda ya bud’e idanunsa dasuke a rufe ba.
Sarkin k’ofar ya amsa da “nine ranka ya dad’e, dama Amintacciyar kuyangar Fulani Ce ke Neman iso”.
Saida yaja guntun tsuka sannan yace tashigo.
Babu dad’ewa saigata kuwa, saida tayi sallama a k’ofar yabata izinin Shiga sannan ta shigo, risinawa tayi (dan ya hanata durk’usa masa saboda ta manyanta sosai) tana fad’in “barka da Safiya ranka ya dad’e”.
Idonsa yabud’e a kanta yace “kin tashi lafiya”.
“lafiya lau ranka ya dad’e, dama Fulani ce tace azo a d’auki yankin jiya”.
Bai fahimceta ba, dan haka yace “miyene hakan?”.
“ka gafarceni ranka ya dad’e, yankin farin k’yallen mutuntaka da aka shinfid’a a gadonka jiya”.
Bakinsa ya ta6e, ya maida kansa ya jingina tareda maida idonsa yanda suke, kusan minti 1 harma ta fidda ran zai amsa, saitaji yace “kije kawai, zan kawo mata da kaina”.
Idanu tad’an zaro waje saboda mamakin zancensa, amma babu yanda ta iya, kowa a masarautar yasan murd’ad’d’en hali irinna Galadima, saidai akwaishi da kirki da yawan k’yauta. ta risinar da kai, “na barka lafiya ranka ya dad’e, afito lafiya”.
Uffan baice mataba harta fice tarufo k’ofar.

Azkar d’insa yacigaba dayi batareda ya maida hankaliba.
Mom ce takirasa a waya, bayan ya gaidata cikin mutunci ta sanar masa gasunan zuwa sashensa suyi sallama, dan jirgin 1pm zasubi ya maidasu tasu masarauta.

Wannan dalilinne yasakashi zuwa Sanar min, amma saiya Tatar ina Waya da fad’in I love you ina kuka kuma, shine yajuya batareda yayi maganaba.

Kamar na sani natashi na gyara gadon fes, nad’anyi shara dukda babu wani datti, toilet nashige nayo wanka.
Ina tsaka da shiri najiwo sallamar da wata murya ketayi tun d’azun, a gurguje na shirya naje na bud’e k’ofar.
Yarane matasa a durk’ushe can gefe a falona, sai wad’anda suka d’an girme musu su biyu.
Ina fitowa suka zube suna gaidani, abinda baka saba ganiba to, duk sai kunya ta kamani, nace “please Ku tashi minene ya faru?”.
“d’aya acikinsu tace “ gimbiya ranki ya dad’e, ki gafarcemu mune masu miki hidima. ni sunana Alawiyya nice mai gyara miki makwancinki kawai da shiryaki, sukuma wad’annan zasu cigaba da sauran hidimominki, irinsu gyaran falo, girki, wanki, baki labari, da sauransu”.
Babbar jaka uba, shirinma sai anmin kamar wata ‘Yar baby, nidai naga idi gaskiya, wannan wace iriyar rayuwacw haka?.
“ranki ya dad’a zamu iya fara aikinmu?”. Alawuyya takuma maimaitawa a aladabce.
Kafin nabata amsa muka jiyo gyaran murya a abayanmu. dandanan naga sun juya suna kwasar gaisuwa, jikinsu har 6ari yakeyi.
Hannu kawai ya d’aga musu, kafin yabud’e baki da k’yar yace, “miya faru ne?”.
Alawuyya takuma rissinar dakai tace, “ranka ya dad’e mune masuma gimbiya hidima”.
Shiru tamkar bazai amsaba, yad’an yamutsa fusaka yana gyara tsayuwa “wanene ya turoku?”.
“ranka ya dad’e mama fulani ne”.
Baice komaiba ya ra6a ta gefena zai wuce ciki, harya kusa shiga sannan yace, “zaku iya tafiya zan nemeku”.
Atare suke fad’in godiya muke ranka yadad’e, ALLAH ya kiyayeka, yatsare bayanka da gabanka.
To tunima yariga yashige, nikam tausayi suke bani wannan abun dasukeyi, nace “please kutashi kuje kawai”.
“to ranki ya dad’e, godiya mukeyi……..
Nidai juyawa nayi nashiga d’akin nima, dan banason wannan kirarin wlhy……………..???

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*??????
*_Typing??_*

*_HASKE WRITERS ASSO…??_*
_(Home of expert and perfect writer’s)_

*_?RAINA KAMA……!!?_*
_{Kaga gayya}_

*_Bilyn Abdull ce????_*

_____________________________

_Wannan page d’in na sadaukar dashi agareki Hafsat writer d’in *HAFEEZ* na gode sosai, ALLAH yabar zuminci, Bilyn Abdull na yinki irin sosai d’inan dear?????????._

______________________________

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply