Farhatal Qalb Hausa Novel Hausa Novels

Farhatal Qalb 69


Farhatal Qalb 69
Viral

PG:69_

_WANNAN LITTAFI DA MA SAURAN NA *ZAFAFA* NA *KUDI* NE. DAN ALLAH KI/KA BIYA KUDI KI/KA MALLAKI NA KI. DON GUDUN SHIGA HAKKOKIN MASU RUBUTAWAR DA MA WADANDA SUKA CIRE KUDI SUKA SAYA…_

_AREWABOOKS👇_

https://arewabooks.com/book?id=63397750fbef002844646ad3

___

Tamkar ba zai tura kofar dakin ba. Sai kuma ya saka hannu ya murda handle din ya shiga ciki. Bakin sa dauke da sallama.

Amsawa tayi. Tana zaune agaban mudubi . Sanye cikin kayan bacci. Ya yinda man kitso ke hannun ta tana mai oiling gashin na ta.

Dan kallon ta ya yi. Hankalin ta na kan abunda take yi. Don haka ya karaci zaman sa. Sai kuma ya mike ya fice.

Yana fita ta juya ta bu kofar da kallo. Ta sauke nannauyar ajiyar zuciya kafin ta mike ahankali cikin sanda tabi bayan sa.

Kofar dakin sa ta nufa .. Har ta saka hannu zata bude kofar sai kuma ta fasa. Ta kasa kunnenta jiyo tamkar muryar sa..

“Kin kwanta ne…..? Uhm? Okay baby. Ki mun kiss sai ki kwanta .No wanka zan na tafi. Wai meye ne kike ta takura na tafi wajen Ahlam? Please ki sa ka wa zuciyar ki hakuri. Ba zata maki komai ba. Ba ki da lefi . Bakisan da aure na ba. Aka auramun ke. Biyayya kawai ki kai wa iyayen ki kike zaune da ni. Tohm. Your wish is my command my princess. Bara na yi wanka na tafi. Muah.” Ya sakar mata kiss daga karshe bayan ya karasa wayar.

Ahlam da ke labe idanuwan ta sun kawo ruwa da sauri ta koma dakin ta. Ta kifu akan gado ta shiga ruzgar kuka. Wace iriyar kiyayya Zayn ya ke mata har haka? Da sai Waheedah ta ce yazo wajenta zai zo? .

Shi kuwa Zayn yana karasa waya da Waheedah ya ajiye wayar yana bin ta da kallo. Kafin daga bisani ya shige cikin bandaki.

Wanka yayo ya shafe jikin sa da turaruka masu dadin kamshi. Ya zura kayan bacci ya fice daga dakin zuwa na Ahlam.

Tun daga bakin kofar yake jiyo shesshekar kukan ta. Hankalin sa ya soma tashi.

Baya kaunar kukan wani saboda raunin da ke cikin zuciyar sa. Ballanta kuma musabbabin kukan saboda shi ne .Bare kuma kukan ma daga mace, Macen ma yar uwar sa. Kuma mata agare shi.

Ya bude kofar dakin cikin sanyin murya ya yi sallama. Tanata rera kuka ahankali da alama ma bata jiyo shigar ta sa ba..

Kukan nata na daza dugunzuma shi. Hadi da karyar masa zuciya. Ya zauna daga kusa da ita.

Ya dan langabar da kan sa saitin inda take kwancen.

“Ahlam….” Ya fadi sunan ta ahankali cikin kulawa .

Bata amsa shi ba. Ta cigaba da kukan. Kanta ya dau zafi. Abun ka da farar mace tuni fuskar ta har tayi ja.

Ya dan sake matsawa daf da ita. Ya saka hannu ya tarota jikin sa ta shiga janyewa.

“Ka rabu da ni. Ka tafi wajen matar ka wacce kafi so da kauna. Daman ita ta tursasa ka ka hawo waje na ai…Ka kyale ni”

Yana karasa jiyo karshen zancen ta ya gano tayi eavesdropping wayar da yake da Waheedah kenan. Hakan ya sashi murmushi.

‘kishi… Mata halayen su sai su’ Ya fada cikin zuciyar sa hade da sosa keyar sa.

Ya rage sautin muryar sa. Cikin kulawa da tarairaya ya janyo ta jikin sa duk kuwa da zame nata jikin da ta ke.

Hannun sa daya na shafa gadon bayan ta. Ya rungume ta tsam a jikin sa. Yana mai hura mata iskar bakin sa cikin wani salo na kwarewa da tarairaya .

“Ahlam…. Dearest wifey na. Ni ya dace nayi fushi da ke fa… Baki mun magana ba at all tun a gidan mu. Sannan na dakko ku a mota na kawo ku. Har ya zuwa nan still baki ce mun ci kan ka ba. Na shigo nan wajen ki kika ba banza ajiya na. Na tafi daki na… Please ki dai na jin haushin Waheedah. Wallahi Waheedah bada masaniyar ta aka auramun ita ba. Waheedah batasan ni ne wanda aka aura mata ba sai bayan an kai lefe ranar da aka daura auren… Har ca tayi na same ki ki umarce ni na rabu da ita. Ba zaki gane ba ne duk yadda zan fada. Amman tana ganin kimarki da dattakon ki da girman ki … Inason ki ajiye a doron zuciyar ki wallahi Waheedah bata ci amanar ki ba. Ahlam na fara kaunar Waheedah tun kafin a daura mana aure da ke. Wannan shine zancena gaskiya. Idan da wanda zaki ji haushi ni ne ba ita ba. Sab…”

“Karka karasa…. Daman na dade da sanin har yanzu babu kauna ta acikin ka…Ka tsane n ….”

Bata karasa ba. Ya hade bakin su waje daya. Duk yadda Ahlam ta so yakice nata. Zayn ya hana. Ta hanyar tallabo fuskar ta da hannun sa. Don bayason yayita bata hakuri ta kalamai. Gwara ya kashe mata jiki gaba daya.

Sai daya ga ji don kan sa tukun sannan ya zare nasa. Yana mayar da numfashi. Hade da sakin murmushi .cikin muryar lallashi yace,

“Uwargidah ran gidah…. Uwargidah sarautar mata. Uwargidah kujerar tsakar gidah… No matter what happens, you will always remain my biggest priority. I promise never to disregard your wishes again. Will you forgive me for what I have done? Ahlam, Wallahi. I never meant to insult you, hurt you, or put you through pain, and I promise to never do this again. I am sorry, please forgive me…Kin yafemun? Uhm? ”

Yana magana yana goga hancin sa akan nata karan hancin. Kamshin turaren jikin su nata dukan hancin su. Ya bada wani sanyayyan kamshi mai matukar sanyaya zukatan masoya.

“I love and miss you…..” Ahlam ta fada tana mai saka hannu akan fuskar Zayn..

“I love and miss you too .” Ya fada yana mai lakuce mata kumatu.

“Ba wani nan…” Ta fada tana dariya.

“Kin manta favourite buddy na ce ke? Tun kafin ki zama mata agare ni”

Ta danyi murmushi. Zayn ya sake janyota jikin sa. Ya gyara masu kwanciya. Ya saka kanta akan kirjin sa. Ya yinda hannun sa ke shafa kwantaccen gashin ta da ke kamshi.

“Ki amince mu yi tsaftatacciyar soyayya. Domin Ahlam, a duniya babu abun da ya kai samun masoyi dad’i, Buri na yanzu bai wuce na ganin hadewar kan ku da Waheedah ba. Zanyi alfahari da ku a duk inda
na kasance…”

Ahlam ta sauke nannauyar ajiyar zuciya. Kafin tace

“Ina kallon Waheedah tamkar Nadra awaje na. Muka sake kusanci ta hanyar dawowar ta gidah na gaba daya. Then all of a sudden ace itace wadda ka auro ? A karkashi na fa ta ke Zayn ”

Zuciyar sa ta dan masa zafin kalamanta na karshe. Amman ya danne ya ce da ita,

“Ai na gaya miki ba wai dawowar ta gidan nan na fara kaunar ta ba. Zan iya ce maki ban san so ba sai akan Waheedah… Sannan Waheedah ba’a matsayin yar aiki aka bamu ita ba kema kin sani. Domin ba biyan ta muke ba…. Ahlam ki fuskanci gaskiyar zance. Dan Allah maganar nan ya kamata ki mata duba na tsakani. Ya kamata ace wadannan abubuwan duk an wuce su. Mu rungumi kaddara.”

“Amma Zayn k…”

Bata karasa ba ya janye ta daga jikin sa zai tashi. Tayi saurin riko shi tana langabar da kai. Domin ita kanta tasan tsawon lokuta data diba bata tare da shi har jinya tayi awajen Ummimi . Tana matukar kaunar Zayn.

“Shikenan nayi shiru…”
Ta fada kanta a kàsa.

Dan murmushi yayi. Ya koma ya kwanta.

“Abunda ya faru haka Allah ya kadarta. Sai fatan Allah ya kara mana zaman lapia da kaunar juna. Hadi da yalwar arziki da wadatar zuci . Ko?”

“Eh….” Ta amsa shi . Tana kallon fuskar sa.

Hannu ya saka ya kashe bedside lamp ya gyara kwanciyar su. Ahlam ta kankame shi sosai tamkar za’a kwace mata shi ..

Daga nan kida ya soma canza salo. Suka shiga bude wasu shafukan na soyayyar su.

Zayn yayi mamakin yadda Ahlam ta ke bashi hadin kai ba tare da kosawa ba kamar a baya.

Nan da nan kuwa suka shiga faranta wa junan su. Zafafan kisses Zayn ya shiga showering jikin Ahlam da su.

Ya kuma ji ta yadda yake muradi. Domin tasha gyara awajen Ummimi. Ta kanas aka dakko mata me gyaran jiki ta gyareta ciki da waje.

Ranar dai saboda tsabar rashin juna da sukayi. Na ramakon kaunar da suka nunawa juna adaren jiya har makarar sallar asubahi suka yi.

××××

Waheedah dakyar ta iya tashi alarm nata dokawa. Taci mamaki da Zayn bai tashe ta ba yau . Allah ya temaka ta seta alarm.

Domin shi ke tashin ta sai kuma ya wuce zuwa masallaci. Amman hakan ya mata dadi gudun tasowar fitna. Kafin Ahlam din taji haushi.

Tanata sauri ta dauro alwala tayi sallah. Ta kwanta akan sallaya bacci ya dan dauketa na yan wasu mintina kafin ta mike ta shige bandaki.

Tayo wanka saboda lectures din safen da zatayi. Ta zura kayanta bayan ta shafa mai. Ta goga hoda sama sama da man lebe bayan ta zizara kwalli

Kitchen ta bude ta shiga. Cikin sauri ta tafasa shayi ta zuba a flask. Ta kai kayan tea din kan dinning area da bread ta ajiye da Nutella/spread.

Tana cikin gyara zaman mayafin ta. Sai ga sakkowar Ahlam din da Zayn a tare. Idanun sa fes akan Waheedah .

Sai sako yake aika mata ta kallon da yake bin ta da shi. Tayi azamar kauda kanta gefe .

“Ina kwanan ku?” Ta gayshe su a tare cikin ladabi

Zayn ya nufeta da sauri yana murmushi. Zai rungume ta ta ja baya da sauri. Ahlam na hankalce da su ta kauda kai gefe

“Zan tafi lectures ne. Ban dade da shiryawa ba. Na kusa makara ne. Ban samu na hada breakfast ba. Sai tea kawai da bread.”

“Sannu da kokari, My Baby.”

Ita dai ta kakaro murmushi kawai. Tayi hanyar fita,

“Na tafi school.”

“Ki jira ni….”

Ya juya wajen Ahlam da ke zaune akan kujera.

“Zan kai ta school …”

“Alright.”

“Daga can zan wuce aiki….”

“Ba zaka dawo ka ci abincin ba?”

Ya dan ja kasan leben sa. Kafin ya daga kai .

“Zan dawo tohm. Bari na kai ta.”

Da sauri ya fice har yana tuntube. Waheedah tayi gaba ta fice daga gate din. Bai tsaya jiran baba mai gadi ya tura gate din da kansa ya futar da motar.

Ya sake rufe gate din bayan ya fitar da motar daga cikin gidan. Tana tafiya ahankali tamkar wadda kwai ya fashewa a ciki.

Ya tashi motar ya tuka har inda take tafiya. Ya zuge glass din.

“Shigo na kai ki …”

Dan kallon sa tayi ta cigaba da tafiyar ta. Zayn abun ya so bashi dariya. Tun baa je ko’ina ba sun fara garashi kamar taya?

Ya daure ya sake bin ta da motar. Ya faka ya fito daga ciki. Yayi taku uku ya riko damtsen hannun ta.

“Nace ki zo na kai ki…. Meya faru ne?”

“A’ina ? Na kawo maka korafi ne?”

Ya girgiza kai alamar a’ah. Kafin ya riko hannunta ya jata har wajen motar ya bude ya sakata ya rufe. Ya koma wajen mazaunin driver ya zauna ya tashi motar.

Yana tuki yana bin ta da kallo.

“Nasan nayi lefi… Koma menene ni dai kiyi hakuri banason kina fushi da ni.”

“Fushi? Meyasa zanyi fushi da kai?”

“Eh to ai ba haka kike mun ba. Baby.”

Ta kauda kai kawai tana turo baki gaba. Ya faka motar a gefen titi yana binta da kallo.

“Zan makara fa…” Ta fada cikin muryar shagwaba.

“Mu tafi kenan?”

“Uhm.”

Ya danyi murmushi tukun sannan ya tashi motar. Suka dauki hanyar makarantar su..

Hannu ya saka ya kunna speaker din motar. Wakar indila ta love story ce keyi ahankali…

“Wifey…I may not be able to say how much I love you or just how special you are to me, but I can say that my world is full of smiles and happiness whenever you are around. I love you with all my heart… Budemin na shigo kofar ZUCIYAr ki , Da sannu zan zamo dauwamammen FARIN CIKIN da zai bunkasa dukkan wani farin cikin rayuwar ki da mu baki daya…. Ki budemun…”

Dan dariya ce ta kufce mata. Ta yi tana kallon sa.

“Me zan bude?”

“Zuciyar ki…. Zan zamo miki *FARHATAL QALB* da zaki gasgata abun da nake fada..”

Hannun ta ta saka ta kare fuskar ta. Har ga Allah kalaman sa na dulmiyata cikin kunya. Har ta rasa ina yake nemo wadannan manya manyan kalaman na hausa..

“Wai meyasa kike jin kunya ta ne..?? Mijin ki ne fa ni… Ba yayan ki ba ”

“Kai Yaya na ne?”

“A’ina na zama Yayan ki?”

“Ya Zayn…”

“Na raba ki da wani Ya Zayn. Ina mjin ki mu gama sharholiyar mu a gidah daya. Daki daya. Gado daya… Ki ce mun Ya Zayn? Noo! Ban karba baa wallahi.”

Dariya ta kyalkyale da ita. Daman kuma dariyar yake son sakata. Don haka shi ma ya murmusa kafin ya sake cewa,

“Allah bana so. Ki sama mun pet name haka. Cuz I won’t accept Zayn or ya Zayn ever again .. ”

“Toh..”

Lakuce mata gefen fuska ya yi. A haka suka karasa cikin makarantar yana ta tsokanar ta.

Ya curo kudin abinci dana handout ya zura mata acikin jaka. Bayan ya bata zazzafar sumba guda daya Tayi masa godiya. Kafin ta sauka ta shige cikin aji

Bayason rigimar Ahlam. Da wajen aiki zai saboda lokaci ya ja Ya koma gidah. Yaci abincin a tsaitsaye .

“Me zaa dafa maka da rana?”

Sai da ya kware don mamaki. Tayi murmushi tana kada kai.

“Kome kika dafa… Less spicy.”

“Alright…”

Tashi yayi ya sumbace ta a gefen fuska . Ya mata sallama ya tafi aiki. Yanata mamakin wai Ahlam ce me tambayar abincin da za’a dafa? .

Cike da farin ciki ya nufi mota ya wuce wajen aiki…Yana jin wata nutsuwa na zagaye shi da annushuwa. Hankalin sa a kwance. Yanata adduar Allah ya tabbatar da wannan zama nasu cikin zaman lumana da kaunar juna da kuma yalwar arzuka…

×××

Rayuwa na ta gudu, Haka zaman nasu ya kasance cikin Alhamdulillah,. Dan kowane rayuwar aure yana da ups and downs dinsa. Waheedah na kokarin bawa Ahlam girma. Ta na kuma bin ta da yadda ta so. Hakan ya sa Zayn ganin tamkar ana kwarar Waheedah. Duba da sai yadda Ahlam ta so take bin ta…

Ga tunkaho da nuna mata gadara da karfin iko akan gidan. Tamkar na ta ne ita daya..

Don haka Zayn ya tunkari mahaifan sa da maganar canzawa Waheedah gidah. Ko zaman lapia zai kara wanzuwa dik kuwa da ahakan ma Alhamdulillahi..

Sun amince da maganar sa. Don raba gidan ma wani kwanciyar hankalin ne. Da dai-daita tsakanin su. Domin wata kazantar da ba ka gani ba tsafta ce.

Nan da nan kuwa farfesa Adams ya ba wa Zayn wani gidah bungalow (flat/marar bene.) Kyauta. Mai kyau da shi a layin su Haj Hameedah din amman daga karshe yake shi ta baya.

Zayn ya saka aka fente masa shi. Aka sake gyara shi sosai. Ya zuba masa kaya masu matukar kyau da tsada.

Ya kuma samu Ahlam da zancen tayi murna kwarai da gaske. Domin tafu kaunar ita kadai anata gidan ta bararraje yadda take so..

Zayn bai gayawa Waheedah ba. Sai ana’i satin da zata koma. Suna zaune a parlour su ukun .

Suna kallon film din titanic. Yana shan fruits din dake gaban sa. Suna hira jefi jefi. Ya ce,

“Kun kasance duk abin da na taba so a soyayya. Kun sanya ni jin ana kaunata ta hanyoyin da ba zan iya tsammani ba. Ba zan taba neman karin ba. Ina son ku da ni tare har abada. Daga yanzu har zuwa numfashi na na karshe, zan ci gaba da kaunarku..Ina son ku sosai ..Na rasa yadda zan yi da son ku har ban san kalmomin da suka dace ba don bayyana abin da nake ji game da ku. Babu wata kalma da zata iya misalta kaunata a gare ku! Na kuma ji dadin yadda kuke mu’amala a yanzu sosai… Har cikin rai na nake jin dadin hakan. Allah kuma ya kara mana zaman lapiya Amin ya rabbi…”

“Amin….” Suka amsa baki daya.

“Ke Waheedah baki sani ba. Amman Ahlam ta sani . Na sanar da ita ..”

Waheedah ta daga kai ta kalle shi ya jinjina mata kai alamar tabbatarwa.

“Nan gidan kamar yadda yake da sunan Ahlam .. Kema Allah yayi na sama maki wani matsugunin wanda yake da sunan ki kema… Amma fa wani hanzari ba gudu ba… Ba bene ba ne flat ne.. Sannan kuma ba anan unguwar ba ne… A tasu Maa ne.” Ya fada yana tsokanar Waheedah daga karshe.

Wani FARIN CIKI ne ya mamaye ZUCIYAr Waheedah da gauraye . Murmushin fuskarta yaa fadada. Kai kana kallon ta kasan taji dadin zancen sa.

Ba dan Ahlam na wajen ba. Har tukwicin sumba ta so ba shi. Sai ta danne dai . Ta shiga godiya agare shi. Zayn yaji dadin hakan kwarai matuka.

Ahlam ma ta tayata farin ciki. Ana’i washegari zata koma Zayn ya kai su gidan su wajen Haj Hameedah da Haj Aisha. Tun safe har rana. Da rana kuma ya dau Waheedah ya kai ta wajen Umman su gidan gwaggo haule. Acan ta karasa wuni har dare.

Washegari kuma akai mata rakiya gidan ta dake nan layin su The Adams family amman daga karshe.

Tsayawa bayyana yadda gidan ya tsaru ma bata lokaci ne. Komai yaji zam zam…. Sai fatan Allah yasa a tsofe lapia yasa kuma an shiga a sa’a.

Ya kuma kawo musu zuriya dayyiba. Domin har yanzu shiru daga Ahlam din har Waheedah. Gashi tuni har zahara’u yar Marka ta haihu. Ba tazara da ke kwanika ta keyi ko auren ta na baya. Shekara na cika ta sake sullubo wani. Ta shiga renon su su biyu .

*GIDAN MALAM NA LADO*

_INA MASOYA KUMA MA’ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._

_TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_

_A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_

_AKWAI TURAREN *AL’AJABU NA TSUGUNNO DA KHUMRAH* DIN SA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN GASHI NA CREAM DA KUMA SPRAY DIN SA NA FESAWA*_

_BA ANAN SUKA TSAYA BA. SU NA DA *TURAREN MOPPING, DA NA BANDAKI AKWAI NA RUWAN WANKI DA NA FESAWA A DRAWER KO AKWATI*_

_AKWAI KAYAN GYARARRAKI NA FATA. KUJERAR TSUGUNNO, KASAKE NA WUTA, COAL IGNITER TA KUNNA GARWASHI, ELECTRIC BURNERS DA ENGLISH COAL_

_AKWAI LAFFAYAS DA SAURAN TURARUKA NA KAMSHI KALA KALA_

_SU NA BADA KAYAYYAKIN SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYA AKAN DAYA DAYA. SANNAN SUNA TURA KAYAYYAKIN SU KO’INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE. KAYAN SU YAN CHADI NE DA SUDAN DA KUMA YERWA WATO MAIDUGURI._

_KYAU, INGANCI DA RAHUSA SAI KAYAYYAKIN KAMFAMIN YERWA INCENSE AND MORE. SAI KUN GWADA ZAKU BAMU LABARI_

_NAMBAR TARHON SU DA ZAA KIRA KO MUSU MAGANA TA WHATSAPP ITACE: 08095215215_

_INSTAGRAM HANDLE DIN SU: @yerwaincense_and_more_

_YERWA INCENSE AND MORE: A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS AND MORE_

❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al’amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K’ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K’ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/23, 9:02 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_
_(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_
💞
_NA_

_NANA HAFSATU_
_(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_

_WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply