Farhatal Qalb Hausa Novel Hausa Novels

Farhatal Qalb 63


Farhatal Qalb 63
Viral

PG:63_

_WANNAN LITTAFI DA MA SAURAN NA *ZAFAFA* NA *KUDI* NE. DAN ALLAH KI/KA BIYA KUDI KI/KA MALLAKI NA KI. DON GUDUN SHIGA HAKKOKIN MASU RUBUTAWAR DA MA WADANDA SUKA CIRE KUDI SUKA SAYA…_

_______

Dake asabar ce. Ya dan jima yana bacci tun bayan da yayi sallar asubah. Yana tashi ya faada bandaki yayo wanka. Hade da yin brush. Ya sauya kayan sa zuwa manyan kaya . Samfurin riga da wando na shadda. Amman bai saka hula ba. Ya dai taje sumar kansa data kwanta luf. Ya kuma taje ta sajen sa.

Ya bulbula turarukan kamshi ajikin sa ya sauka kasa. Babu Ahlam a duk wani daki da parlorn da ke kasa. Ba kuma ta kitchen ba ta farfajiyar waje. Hakan ya bashi damar ganowar tana sama.

Don haka ya koma saman. Tana cikin dakin ta. Ya murda ya jita a datse alamun ta saka makulli. Har zai juya sai kuma ya tsaya jiyo wayar da ta ke a handsfree ne kuma da aminiyar ta Bushra suke wayar. Don ya gano muryar. Ahlam din na kuka tana daga sautin muryar ta. Wayar sa ya janyo. Ya danna wajen recording ya seta ta.

“Wallahi ita dai Bushra… Ko a mafarki ban taba kawowa yarinyar nan itace wadda Zayn zai auro ba.. Bushra Zayn ya cuce ni.. Ya gama da rayuwa ta. A iya tsara rayuwa ta da nayi wallahi ban taba kawowa Zayn zai mun kishiya ba…Ya illata ni.. ”

“Kiyi hakuri bestest ..Shawarar dana baki dai itace final solution.. Itama yarinyar ai na gaya miki ba ta zauna ba. Bare sunga gidan dadi ne. Ita da mahaifiyar ta zasu bazama bokaye su dasa soyayyar ta acikin zuciyar sa. Ina Zayn ina wannan kucakar yarinyar? Ita ba wata kyakkyawa ba . Dan wallahi kin fita kyau, Ita ba class ba. Ita ba wadataccen ilimi ba. Ba kuma daga babban dangi tafuto ba na mulki ko sarauta.. Ai ke kina ganin lamarin kinsan asiri ne ba yin kansa ba ne. Soyayyar jinnu ce. Ai shiya sa gwara da kika kaurace masa. Kika hanashi kusantar ki har sai ya dawo cikin hankulan sa…”

“Gaskiya nima nayi wannan tunanin da farko. But babes lamarin fa babba ne. Allah tun lokacin bikin mu bana gaya miki ba? Ya kira ni da Waheedah, Nace Waheedah kuma? Ko bayan auren ma. Tunda ta dawo nan gidan. Yanayin yadda yake bin ta da kallo zaki gane he’s into her.”

Zayn ya girgiza kai kawai. Ya sake gyara tsayuwar sa. Yana mamakin sakarci irin na Ahlam da ke bin zugar kawaye . Meyakwan tayi kokari ta gyara rayuwar auren ta dake neman tabarbarewa.

Ji yake tamkar ya dakko spare key ya bude kofar. Ya shiga ya kashe wayar ya kuma buga ta da kasa. Saboda tsananin yadda zuciyar sa ke tunzura shi.  Ya dakata kawai.

“Kibar aikin bokonci Ahlam. Na ke gaya miki. Kaunar da yake miki hatsabibin bokan su ya dauke ya dasa a zuciyar Waheedah din. Shine ya mato akanta. Tsinannu. Nagaya miki na samo hanya. Sha yanzu magani yanzu. Aikin sa kamar yankan wuka yake. Idan ma so kike ya rabata da iska. Zai kashe ta. Ta hanyar mata turen ciwo. Ko ya haukata ta. Ko ya mata kurciya ta shiga duniya a nemata a rasa. Ko a saka mata mantau ta manta komai nata…. Ko”

“Noo bestest…. Duk bana kaunar wadannan abubuwan. Kar a mata ko daya daga ciki. Banda kisa, Banda hauka, Banda mantau din da kikace banda kuma kurciya din. If there’s no other way.. Mu hakura kawai.”

“Ke dai wani lokacin banza ce wallahi. Tazo har gidah ta shiga jikin ki.. Ta aure miki miji kice duk wadannan ba zaki iya ba? Kar ki manta ta kaudar da hankalin mijin akan ki . Ni gidan ki da tazo ta zauna ma tun farko bai kwanta mun ba… Saboda nasan da wata kulalliyar tazo. Maybe ta dauki kayan sawar ki ma ta kai da su akai amfani. Ke wasu mutanen fa mugaye ne. Da kuma na gaya miki nace mahaifiyar sa bata kaunar ki. Har da ita a masu ruwa da tsakin..”

“Ai nima da kika fada na gano haka ne. Bata kaunata. Tana wani murmushin mugunta. Daman can ita ta hada auren. Tunda agidan ta suke aiki yarinyar da mahaifiyar ta. So ni dai yanzu so na ke yarinyar nan a lalata rayuwar ta kawai taji batason zaman auren ni yafiye mun. Shi ma yatsaneta.. Kingane?”

Zayn ya kara harzuna. Gumi na keto masa na tsananin bacin rai. Ya danne ransa. Yana jiyo sanda Bushra ke ce mata,

“Zan gayawa bokan kan ya shafe gaban waheedan. Kar ma Zayn din yaga komai idan yazo auratayya da ita. Ya shafe shafin siminti (cement) Ya kuma cire kaunar sa a zuciyar Zayn din ta zama itace bakin cikin sa a rayuwa. Sannan ya kara mata da warin jaba. Ta dinga hamamin doyi. A kuma cire kaunar da yake mata . Da shi da mahaifiyar ta sa. Ke long story short shi ma a rabashi da mahaifiyar ta shi. Ya juya mata baya. Ta yadda ke kadai zai dinga jin maganar ki. Ya kuma saki Waheedah din. Ya zama ya dawo a tafun hannuwan ki. Sai yadda kikayi da shi . Koya kika ce?”

Ahlam ta kyalkyale da dariya har tana kyakyatawa tamkar ba ita ke kuka dazu ba.

“Sha kurumin ki. Ki bar zubar da hawayen ki. Hanyar gidan boka ba wanda bamu sani ba. Kede kawai dukkanin umarnin daya ketara miki kiyi . Ko sallah yace ki bari ta yan kwanaki ce kingane? ”

“Nagane kawata… Na gaya miki banda kisa dai. Banda dik sauran. Kawai a shafe gaban nata a kuma saka mata doyin. A kuma cireta a ransa. Sannan yadda kikace din. Na aminta .A raba shi da mahaifiyar tasa. Daman yadda yake kaunar ta yana ci mun tuwo a kwarya . Komai Maa. Komai Maa. Sai abunda tace. Kullum yana can wajenta na tsani hakan. ”

“Sha kurumin ki. Tamkar an raba su ne. Ina nan shigowa dana harhada komai zan je wajen sa. Da kai na zan biyo flight na zo. Na gaya miki aikin sa kamar yankan wuka ya ke. Zan hado miki da wanda Zayn din zai bude miki bakin aljihun sa ma. Duk kudaden sa ke zaki rika juyawa. Ki kuma mayar da shi rakumi da akala sai yadda kikayi da shi. Ta yadda idan kika ketara kara ba zai tsallaka ba. Idan kikace da bakin abu fari. To ta zauna.. kawata.. ki kokarin samun tufafin su ki aiko ko da ta tasha ne.. ”

“Masha Allah tawaje na. Amanar zuciyata. Bugun numfashin senator gallauro.. Allah ya biya ki da alkhairin sa. Ya yi auren ku da sanata.”

“Amin kawata…. Sai na kira ki ”

“Yauwa.. Godiya na ke.”

Suka katse wayar da suke yi. Yana jiyo sakin karar farin cikin da Ahlam tayi tana buga kafafu

Kasa tabuka komai yayi. Ya yin da kafafun sa suka gaza daukar sa. Ya jingina da bango yana runtse idanu. Maganganun su Ahlam sai yawo suke masa a kwakwalwa.

Innalillahi wa inna ilaihi rajiun… Ya shiga maimaitawa yana mai dafe goshin sa da jijiyoyin sa suka daga saboda tashin hankali.

Dakyar ya iya mikewa ya sauka kasan. Kai tsaye ya wuce wajen freezer ya dakko ruwa ya zauna ya sha. Tukun sannan ya fice daga gidan bayan ya shiga mota.

Gidan su ya nufa kai tsaye. Haj Hameedah ya samu a karamin parlor tana karatun jaridah. Bayan sun gaysa ne take tambayar sa ya Ahlam da fatan dai zaman su ba matsala?

Ta lura ainun da damuwar da ya shiga don haka ta shiga tambayar sa akan me ke faruwa? Ya kasa boyewa saboda gudun faduwar abun Allah ya kyauta. Don haka ya janyo wayar sa ya kunna mata recording din da yayi na hirar Ahlam da kawarta.

Haj Hameedah ta saurara gaba daya tana kada kai. Ta tsorata da mamakin yadda suna kananun yara amman suke kokarin kulla wannan mugunta haka? Don haka bata tsayar da zancen ba.

Ta tasa Zayn agaba suka tafi sashen Abiey dinsu. Allah ya temaka ma su Ummimi sunzo tare da sauran iyalan nata. Bayan sun gaggaysa. Ummimi na tambayar Zayn Ahlam. Maa ta bashi umarmin daya kunna musu recording dinnan domin abun yafi karfin ta

Don haka aka samu babban music player aka hada ta da wayar aka kunna yadda kowa zai saurara dakyau. Hirar su tafara tiryan tiryan. Parlorn ya dauka da salati da sallallamin girman maganganun da suke futowa ta recording din.

Ummimi ta shiga girgiza kai kawai tana mai kambama mamakin zantukan. Suna karasa saurara kuwa ta sa lalle a je a dakko Ahlam . Hakan kuwa akayi. Basher aka tura ya dakko Ahlam din. Tanata tambayar sa daukowar menene? Yace su Ummimi ne zasu gaysa.

Ko da ta shiga parlorn. Hada gaisuwar tayi ta jimlanta. Suka amsa baki daya. Banda mahaifin ta. Da yake jefa mata kallo mai tattare da bakin cikin abunda tayi. Yana mai tir da munanan halayen ta.

Ummimi ta saka Ahlam din ta dawo gabanta. Bayan tayiyyi nasiha mai ratsa ta shiga cewa,

“To ma menene auren? Don naga tamkar baki sani ba. Aure shine hada wata irin alaka tsakanin mace da namiji , wannan yana nufin hade rayuwarsu su zama daya, haka nan kuma makomarsu ta zama daya. Kowace irn al’umma akwai irin matsayin da ta bawa aure a musulunci wani dauri ne da yake halattawa ma’aurata {mata Da miji) jin dadi a junansu ta hanyar saduwa da kuma sauran muamaloli, ALLAH (SWT) ya halicci mace daga hakarkarin namiji ya kuma sanya soyayya da tausayi a tsakaninsu (kamar yadda ya gayamana a alkur’ani mai tsarki ). Wannan yana nun mana cewa alaka tsakanin mace da namiji ALLAH ne ya kulla tun fil’azal. Abin da ALLAH kuwa ya hada babu mai rabawa . wannan shine yasa a dabi’ance kowa ne namiji yana bukatar mace, haka kuma kowace mace tana bukatar namiji. Wato ko wane daya bazai iya wadatuwa dakansa ba, ya rayu shi kasai dole ne sai da wanin sa.

“ALLAH (SWT) da ya sanya wannan danga ta tsakanin mace da namiji bai barsu haka nan kara zubeba , suyi ta saduwa barkatai ba tare da wani tsari ba.saboda idan abin ya zama haka tsarin rayuwar yan adam zai wargaje. Domin kuwa za ai ta samun“yaya barkatai batare da masu daukar nauyinsu ba. Don kuwa basu da wani uba guda daya tsayayye wanda zai dauki dawainiyarsu. Wannan zai sa rasa tausayi tsakanin alumma, domin kuwa babu wani wanda zai nuna cewa akwai wata alaka ta jinnu tsakaninsa da wani wanda har zaisa ya rinka jin tausayinsa yana raga masa. Saboda haka ALLLAH ya hallata aure tsakanin mace da namiji, ya zama kuma cewa aure sunnace guda ta annabi ce da take wajibi a wajen duk mai iko yayi shi. Kuma yazama dole kafin ayishi sai anyi sadaki da waliyai da kuma shaidu. Sadaki yana nufin ladan da zaa baiwa mace saboda halarta farjinta, kasancewar kuma mace bata aurar da kanta , ya zama dole asamu waliyi (mahaifinta ko danginta maza ko alkali ko sarki) da zai aurar da ita. Wannan zai iya zama garkuwa gareta daga wulakanici da zai iya yiwuwa mijinta yayi mata. Shaidu kuwa, domin su shaida kulla dangantaka aure tsakanin maauratan domin kiyaye da yin shaida kan dukan wani hakkoki da suka rataya da aure, zuriya da sauransu.Musulunci addini ne da ya kunshi komai da komai don inganta rayuwar dan Adam a duniya da Lahira.

“Bai bar dan Adam ya yi amfani da hankali da tunaninsa kawai don tsara wa kansa makoma ba, saboda shi dan Adam mai rauni ne, mai son zuciya ne, mai hadama ne, mai rowa ne, kai karewa ma mai butulci ne ga wanda Ya halicce shi… Astagfirullah, To in har zai yi butulci ga Mahaliccinsa, ta yaya zai tsara rayuwar da sauran abokan zamansa za su ji dadi?

“Aure daya ne daga cikin ginshikan rayuwar al’umma, wannan ya sa Musulunci bai bar shi sasakai ba ka’idoji da dokoki ba. Kuma baya ga ka’idojin zamantakewa a tsakanin ma’auratan, duk da ba a fata, amma ya tsara yadda za a rabu idan aka kasa samun jituwa ko maslaha a tsakanin miji da matar. A cikin Alkur’ani Mai girma a Suratul Bakara Aya ta 221. Allah Madaukaki Yana cewa: “Kuma kada ku auri mushrikai mata (arna), har sai sun ba da gaskiya. Hakika baiwa mumina ta fi mushrika koda ta kayatar da ku. Kuma kada ku aurar wa mushrikai maza wadanda kuke yi wa walicci, har sai sun ba da gaskiya. ‘Hakika bawa mumini ya fi kafiri, koda (kafirin) ya kayatar da ku.

“Wadancan suna kira ne zuwa ga wuta, Allah kuma Yana kira ne zuwa ga Aljanna da gafara da izininSa. ‘ tsarki, amma duk sauran abubuwa sun halatta su yi da su. 223. “Matanku gonakinku ne, sai ku zo wa gona kinku ta inda kuka so, kuma ku gabatar da (basmala da hamdala da addu’o’i na alheri) don kanku, ku ji tsoron Allah, ku sani hakika ku masu gamuwa da Shi ne. “Kuma ka yi wa muminai albishir “dakyakkyawan sakamako).” Hadisin Annabi (SAW) da Buhari ya ruwaito ya ce, “Dukkan abin haihuwa an haife shi ne a kan tafarkin Musulunci, sai dai iyayensa su mayar da shi Bayahude ko Banasare ko Bamaguje. ki sani, allah Mai ji ne, Masanin abin da kuka fada ko kuka aikata… Kina saurara na?”

Ahlam ta dan juyar da kan ta. Ummimi ta zura hannu ta kwace wayar da Ahlam din ke kokarin boyewa bayan ta gama chatting. Ta cigaba da cewa,

“Bana jin kinsan hakkokin miji akan matar sa, An karbo daga Abu Hurairah (RTA) yace: Manzon ALLAH (SAW) Yace: dan mutum ya kira matarsa zuwa ga shimfidarsa amma bata je masa ba, sai ya kwana (a wannan daren) yana fushi da ita, Mala’iku za suyi ta la’antarta har (zuwa) wayewar gari». Bukhariy da Muslimne suka rawaito shi.

“A wata ruwayar ta su kuma:; «Idan mace ta kwana tana mai
kauracewa shimfid’ar mijinta, Mala’iku za suyi ta la’antarta har (zuwa) wayewar gari»A cikin wata ruwayar kuma: Manzon ALLAH (SAW) Yace: «Na rantse da wanda rai Na yake hannunsa, babu wani mutum da zai kira matarsa zuwa ga shimfidarsa kuma sai taki zuwa gareshi, face wanda Ke cikin sama Ya yi fushi da ita har sai
(mijinta) ya yarda da ita»
A cikin wannan Hadisi: “akwai dalili mai karfi akan haramcin
bijirewar mace dan mijinta ya bukace ta zuwa ga mu’amalar
aure, domin cewa lallai fushin ALLAH zai tabbata a gareta, a tare da haka kuma akwai la’antar Mala’iku”.Wajibi ne mace ta zamo mai kokari wajen sauke hakkokin
mijin ta akanta daidai gwargwado ba tare da jinkirtawa ba, ko
a sanya sharuda ko sharadin sai ya mata wani abu ko ya
bata wani abu wannan haramun ne, matukar dai tana halin lafiya, wajibi ne akanta ta sauke hakkin mijin ta musamman
hakkin mu’amalar aure duba da in taki amincewa hakan zai
cutar da shi ya iya jefa shi cikin hali na damuwa ko sabon ALLAH.Manzon ALLAH (S.A.W) Yace; Idan namiji ya kira matar shi ga bukatar sa to taje masa ko da tana kan tanda ne [Tirmidhi]
Wannan hadisin; Dalili ne akan wajibcin da’a ga miji musamman da’a mu’amalar aure, kuma yana nuni mace ta
gabatar da da’an akan shagalgalun ta.
Shima kuma miji wajibi ne gare shi, matukar yana ha’lin lafiya ya amsa kiran ta in ta bukace sa, domin dukkan su masu hakki ne akan junan su, rashin bata hakkin ta itama zai cutar
da ita ya iya Kaita ga sabon ALLAH, ALLAH ya tsare…

“Haka zalika ki sani aljannar ki tana karkashin kafar mijin ki. Duk kaurace masa da kike a shimfida da kuma kin ladabci agare shi da kula da shi. Lalle kina tattare da fushin mahaliccin ki. Tunda baliga ce ke. Kinsan gaskia kinsan akasin ta Ahlam . Ki sani shirka babbar abace . Domin kuwa hada Allah da wanin sa ne. Bayan Allah buwayi ne gagara misali. Bai haifa ba. Kuma baa haife shi ba. Ba shida kishiya ba kuma ya son a màsa kishiya. Kin dau sirrikan ki komai da komai kina gayawa kawar ki saboda ke din bakida hankali Shashasha ce kuma sakarai lamba daya. To ki sani daga yau wallahi babu hannuna a auren ki da Zayn. …”

Da sauri Ahlam ta kalli Ummimi.

“Saboda me Ummimi?”

“Saboda bakida hankali. Auren ku ya zo karshe ni dai awaje na. Don ba zaki cutar da su ba. Wallahi kinji na gaya miki. Dan uban ki baa kara auren aka auro mahaifiyar ki? Ko ita kadai kika tashi kika gani agidan ku. ? Wacce bakar mummuna kuma muguwar rayuwa kika daukawa kan ki? Duk akan ya karo aure? Ke dai bakida mutunci.”

Kawai Ahlam ta fashe da kuka.

“Ummimi amana ta yaci fa. Ya rasa wadda zai auro sai Waheedah dana rika a matsayin yar uwarta kanwa ta ta jini Ummimi? Taya zanyi zaman kishi da Waheedah Ummimi? Taya? Meyasa Zayn zai munafurce ni ya auro Waheedah Ummimi? ”

Ummimi taja tsaki. Kafin tayi kwafa tana kada kai. Cikin hasala tace,

“Halayen ki .. Su suka fara nesanta ki daga zuciyar Zayn. Bakida kirki Ahlam . Summimi kasau ce ke. Mai bin Shawarar kaawaye . Gashi kawar ta kai ki ta baro ki. Kafata kafarki kinji na gaya miki. Dukkanin hirararakin naku da kawar taki duk mun saurara. Zakuje wajen boka ko da zai lalata rayuwar Waheedah. Ta fita daga gidan Zayn. Ku kuma raba Zayn din da mahaifiyar sa data kawo shi duniya. Sannan ku mayar shi saniyar tatse da rakumi da akala sai yadda kikayi da shi ko? Yar banzar yarinya yaushe har kikasan wadannan mugayen alkaba’en.? Ki auri mutum da hakoran sa 32. Da mahaifiyar sa da ta dauke shi wata 9 ta haife ta shayar da shi har girman sa ki ce zaki raba su? Haka zalika Allah ya hada auren sa da Waheedah. Yarinyar da biyayya tayi ba zabin ranta ba aka aura masa ita kice ta ci amanar ki zaki salwanta rayuwar ta? Karya kike wallahi. Ba boka da ke aiki kamar yankan wuka ba. Kinsan Allah kinga wayar nan daga yau tabar hannun ki. Ke da ki sake saka yarinyar nan kawar ki a idonki ko kuyi magana a waya sai ranar da Allah yayi da rabo. Amintar ku ta kare wallahi. Ba bu ke babu ita. Auren ku kuma bazai bata zumunci ba wallahi. Dole a hakura da shi. Idan kinyi hankali inda rabo kya dawo. Amman dai yanzu ya kare. Tunda ba kaunar sa kike ba…”

“Wallahi Ina kaunar sa.”

“Kina kaunar tasa kike Shan magungunan hana daukar ciki? Matar da bata son karuwa da mijinta ai ba mata bace. Ko kuwa?”

Ta juya tana kallon yan parlorn. Suka amsa baki daya. Dukkanin su ransu ba dadi. Mahaifin Ahlam ya tashi a zuciye. Gamin yadda take bin Ummimi da wani kallo. Ya wanke kuncinanta da mari har hudu. Tamkar ruwan taurari me hatsihatsi haka Ahlam ta shiga gani tsabar gigicewa da zafin marukan. 🤣

“Marar mutunci. Shashasha. Sokuwa kuma sakarai marar kwakwalwa. Ki sunkuya ki bawa Ummimi hakuri kuma ki bawa Haj Hameedah hakuri dan uban ki…. Wannan da haihuwar ki gwara a …”

“Dan Allah kar ka karasa. Ka dubi girman Allah ..” Ummimi ta hana shi.

Haka dai suka tasata agaba. Kowanne yana tofa albarkacin bakin sa. Me fada nayi me zagi nayi. Kowanne dai sai da ya tsawatar wa Ahlam

Wunin ranar baki daya akan Ahlam ya kasance. Har dare bayan anyi sallah. Jan kunnen suka cigaba da yi. Daga karshe aka karkare akan tafiya da Ahlam .

Ummimi ta tasata agaba suka tafi. Kan idan ta kintsu zaa dawo da ita. Idan kuma akwai sauran daga to auren su da Zayn ya kare. Don basa san zumuncin ya rabu shi ya saka suke bin zarcewar umarmin sannu ahankali…..

#DeStInEd LoVe…💕
_INA MASOYA KUMA MA’ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._

_TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_

_A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_

_AKWAI TURAREN *AL’AJABU NA TSUGUNNO DA KHUMRAH* DIN SA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN GASHI NA CREAM DA KUMA SPRAY DIN SA NA FESAWA*_

_BA ANAN SUKA TSAYA BA. SU NA DA *TURAREN MOPPING, DA NA BANDAKI AKWAI NA RUWAN WANKI DA NA FESAWA A DRAWER KO AKWATI*_

_AKWAI KAYAN GYARARRAKI NA FATA. KUJERAR TSUGUNNO, KASAKE NA WUTA, COAL IGNITER TA KUNNA GARWASHI, ELECTRIC BURNERS DA ENGLISH COAL_

_AKWAI LAFFAYAS DA SAURAN TURARUKA NA KAMSHI KALA KALA_

_SU NA BADA KAYAYYAKIN SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYA AKAN DAYA DAYA. SANNAN SUNA TURA KAYAYYAKIN SU KO’INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE. KAYAN SU YAN CHADI NE DA SUDAN DA KUMA YERWA WATO MAIDUGURI._

_KYAU, INGANCI DA RAHUSA SAI KAYAYYAKIN KAMFAMIN YERWA INCENSE AND MORE. SAI KUN GWADA ZAKU BAMU LABARI_

_NAMBAR TARHON SU DA ZAA KIRA KO MUSU MAGANA TA WHATSAPP ITACE: 08095215215_

_INSTAGRAM HANDLE DIN SU: @yerwaincense_and_more_

_YERWA INCENSE AND MORE: A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS AND MORE_

❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al’amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K’ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K’ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
[11/23, 9:02 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_
_(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_
💞
_NA_

_NANA HAFSATU_
_(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_
_WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

 

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply