Farhatal Qalb Hausa Novel Hausa Novels

Farhatal Qalb 48


Farhatal Qalb 48
Viral

_PG:48_

_WANNAN LITTAFI DA MA SAURAN NA *ZAFAFA* NA *KUDI* NE. DAN ALLAH KI/KA BIYA KUDI KI/KA MALLAKI NA KI. DON GUDUN SHIGA HAKKOKIN MASU RUBUTAWAR DA MA WADANDA SUKA CIRE KUDI SUKA SAYA…_

__

*GIDAN MALAM NALADO*

*Waheedah* na tsakar gidan su tanata share share. Kawayen ta suka shigo bakunan su dauke da sallama. Tsantsar farin ciki ya bayyana a fuskokin su.

Tana ganin su ta tsaya da sharar. Ya yinda tsintsiyar ke hannun ta na dama. Kallon su take tana son magana ta kasa .

Basira da fanna suka sheke da dariya. Cikin tsantsar farin ciki marar misaltuwa suka rungumeta a tare.

Ta cillar da tsintsiyar hannunta ta kankame su. Cikin muryar zakuwa ta dube su,

“Ya ake ciki…? ”

“Kin samu admission Waheedah .. kin samu.” Fannah ta fada tana mai sake kankame Waheedah cikin farin ciki.

“Waheedah sunan ki ya fito.kin tsallake….”Basira ta fada tana dariya itama.

Waheedah ta dubi gabas tayi sujjada. Hawaye daya na bin daya na farin ciki

“Allah ka karawa annabi daraja, Aamin. Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillahi da’iman wa Abadan. Allah mungode maka da wannan babbar kyauta…. Ni Waheedah na samu nursing…? Rabbi ka dafa mana ka iya mana….. ”

“Aamin . Amin” suka hada baki wajen amsa adduoin ta…

Inna Sa’adatu dake leken su ta window ta tabe baki ta koma ta kwanta akan katifa tana jera tsaki.

Mikewa tayi ta sake rungemu su kafin ta saka kasan rigar ta tana goge hawayen dake zuba. Cikin farin ciki ta sake cewa da su,

“Nawa kawai ku ka fada …. Ku fa? Sai kace ni kadai ce ke neman admission din? ” Ta jefe su da hararar wasa.

Fanna ta tuntsire da dariya sannan tace,

“Muma duk mun samu…”

Sake rungume juna sukayi sunata murna. Cikin haka Marka da Deluwa suka shigo.

“Ife ifen menene haka har waje ana jiyo shewar ku?”

“Mun ci jarabawar shiga makarantar school of nursing …”

“Ah masha Allah…. Allah yasa ku fara a saa ” Deluwa ta amsa su tanata murmushi.

Domin babu lefi suna mutunci da Waheedah. Ita kan tayata aikin komai idan tazo kwana. Da sauran hidindimu da ke deluwan ta samu karuwa juye ne batayi ba. Cikin har ya dan tasa. Kuma kullun tana basu abinci har da Najib.

Marka ta ja tsaki tana yamutsa fuska.

“Sai kuyi tayi ai… Boko ko jaraba. Bokon ce agaban ku ba aure ba. Gandama- gandama da ku. Meya kwan ku rufawa junan ku asiri ku tsaida mazaje kuyi aure? Kun gwammace ku yita yawo a titi da sunan karatu. Allah shi kyauta.” Ta shige cikin dakin ta tanata doka mita.

“Aunty akwai abunda zan tayaki da shi ?” Waheedah ta tambayi Deluwa.

“A’ah Waheedah… Babu komai”

“Tohm..”

Daki tayi saurin shigewa. Najib yana kwance akan katifar sa. Ya yin da hannun sa daya ke kan kafarsa yana matsawa.

“Sannu Najib…”

“Yauwa Yaya..”

“Kana sauraron mu ko?…..” Ta karasa tanbayar sa tana murmushi..

“Yanzu na tashi …”

“Sannu…. Ya jikin naka?”

“Da sauki..”

“Allah ya kara sauki . Amin”

“Amin..,”

“Na samu admission fa ..”

Mikewa yayi daga kwancen da ya ke. Fuskar sa lullube da farin ciki.

“Har na hango ki cikin farin uniform dinnan…”

“Kai de bari Najib… Alhamdulillah.”

“Na tayaki murna Yaya… Allah ya cigaba da kara miki nasara. Ya bada sa’ar karatu.”

“Amin Aamin ..”

“Umma ta sa ni?”

“A’ah yanzu na ke son zuwa na gaya mata… Bansamu naje na dubo ba… Su Basira ne ke sanar mun”

“Masha Allah … Alhamdulillah.”

Kayan ta ta ciro da ke cikin wata leda viva. Ta fice wajen tana,

“Kuyi hakuri kawayen amana…. Bari na sauya kaya ”

Dakin su Zainab ta shiga ta sauya kayan. Ta shafe jikinta da mai. Ta goga ruwan alumun a hammatar ta.

Sannan ta shafe jikinta da turaren ruwa. Duk sanda ta shafa ko ta dauki kwalbar sai ta tuno yayan su marigayi Kamal.

Yanzun ma hakan ne ya kasance. Siraran hawaye suka zubo mata kan fuskar ta. Ahankali cikin rawar murya tace,

“Allah ya jikan Yaya Kamal.. Rabbi ka gafarta masa. Ka shayar da shi ruwan alkausara. Rabbi kasa yana aljannatul firdwas madaukakiya da shi da sauran musulmai baki daya, Amin ”

Da sauri ta karasa adduoin ta sauya kayan nata zuwa wanda ta dakko. Bata wani tsaya kwalliya ba. Ta dai shafa farar hoda da man lebe.

Ta yi daurin dankwalin channel o. Ta yafa wadataccen mayafin da Umman su ta bar mata.

“Muje…”

“Kawata kina lokaci. .” cewar Basira.

“Kece me yin lokaci tawan…” Waheedah ta fada tana murmushi.

“Gaskia Basira ta fada… Kina kamshi muna bin ki da humra. Kinga yadda kika tsatso kyau tawan? Sai ma a uniform. ” Fannah ta fada tana dariya

Ita dai Waheedah murmushi kawai take. Tayi wa Deluwa sallama suka fice bayan ta sake duba jikin Najib.

“Ni fa gida zan wuce ….” Basira ta fada .

“Kai kawata….”

“Allah tafiya .kawata ”

“Eh kinsan ni kadai ce basu dawo ba .”

“Eh kuwa.”

“Nima dai tafiyar zanyi. Zan tsaya shagon Na’Ateeku na sayo cefanen da Umma ta bani.”

“To shikenan… Idan na dawo zaku jini. Godia nake kawayen amana .. Allah ya albarkar ci zumuncin mu. Aamin”

“Aamin Yaa rabbi .”

“Aamin Aamin .”

Mikewa tayi kanta tsaye zuwa hanyar new gra shurah inda gidan aikin Umman su yake.

Ta dade bata je ba . Rabon ta da zuwa tun suna rubuta jarabawar kare sakandire.

Bakinta dauke da adduoi ta karasa shiga layin. Manya manyan motoci suna fa ke a kofar gidajen unguwar. Kanta tsaye ta shiga cikin gidan na The Adams Family….

Taci saa kuwa kofar sashen baa kulle take ba. Wata mai aiki tafuto daga cikin gidan tana tattare kofar.

“Sannu Ina wuni…?”

“Lapia kalau…. ”

“Ya aiki?”

“Alhamdulillah….. Ki shiga suna ciki.”

“Tohm…” Ta amsata cike da ladabi.

Ta kutsa kai ciki bakinta dauke da sallama.

“Wa’alaykm Salam…. Ahhh wata sabon ga ni…” Nadra tafada tana mikewa tsaye..

Bata da kyama ko ganin kaskancin na kasa da ita.

“Ina wuni sis….?”

“Alhamdulillah…dear sis.”

“Maa ga Waheedah… Umma ga Waheedah..”

Daga kitchen suka fito a tare. Haj Hameedah da Umma Hadiza. Fuskokin su fadade da murmushi.

Ta tsugunna har kasa ta gayshe da su. Suka amsa duka fuskokin su a sake.

“Lapia lau…… Waheedah na.” Maa ta fada tana murmushi.

“Alhamdulillah…..” Umma Hadiza ta amsa ta.

“Je ga abinci can a dinning ki zuba kici.” Haj Hameedah tace da ita.

“A koshe naki Maa.”

“To kya tafi da shi… Kwana biyu kin manta da mu. Sai yau?”

“Tuba na ke Maa…”

Zama tayi tanata lankwasa hannayenta kafin ta sake cewa,

“Na samu admission a school of nursing…….

_INA MASOYA KUMA MA’ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._

_TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_

_A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_

_AKWAI TURAREN *AL’AJABU NA TSUGUNNO DA KHUMRAH* DIN SA_

_SANNAN SU NA DA *TURAREN GASHI NA CREAM DA KUMA SPRAY DIN SA NA FESAWA*_

_BA ANAN SUKA TSAYA BA. SU NA DA *TURAREN MOPPING, DA NA BANDAKI AKWAI NA RUWAN WANKI DA NA FESAWA A DRAWER KO AKWATI*_

_AKWAI KAYAN GYARARRAKI NA FATA. KUJERAR TSUGUNNO, KASAKE NA WUTA, COAL IGNITER TA KUNNA GARWASHI, ELECTRIC BURNERS DA ENGLISH COAL_

_AKWAI LAFFAYAS DA SAURAN TURARUKA NA KAMSHI KALA KALA_

_SU NA BADA KAYAYYAKIN SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYA AKAN DAYA DAYA. SANNAN SUNA TURA KAYAYYAKIN SU KO’INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE. KAYAN SU YAN CHADI NE DA SUDAN DA KUMA YERWA WATO MAIDUGURI._

_KYAU, INGANCI DA RAHUSA SAI KAYAYYAKIN KAMFAMIN YERWA INCENSE AND MORE. SAI KUN GWADA ZAKU BAMU LABARI_

_NAMBAR TARHON SU DA ZAA KIRA KO MUSU MAGANA TA WHATSAPP ITACE: 08095215215_

_INSTAGRAM HANDLE DIN SU: @yerwaincense_and_more_

_YERWA INCENSE AND MORE: A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS AND MORE_

❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥

*_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al’amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_*

*_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_*

*_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K’ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_*

😄😄😄😄😄😄😄

*YA KUKAJI SALON MASU KARATU?*

*YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA*

INAYA(riba biyu)___mamughee

SANADIN LABARINA___Rano

BABU SO___Billynabdul

FARHATUL K’ALB___Miss xoxo

GURBIN IDO____Huguma

*ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?*

*_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_*

Biyar:::1k
Hudu:::700
Uku::::500
Biyu::::400
Daya:::300

*_zaki saka kudin ta wannan account number din_*

HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Zenith bank

*Saiku tura shaidar biya zuwa ga*
07040727902

*IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR*
09134848107

*_THANKS FOR THE CONTINUED PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰[11/23, 9:02 PM] Mummyn Yara: _*FARHATAL-QALB*_
_(FARIN CIKIN ZUCIYAH)_
💞
_NA_

 

_NANA HAFSATU_
_(MX)_

_AREWABOOKS:MISSXOXO_

_WATTPAD: MISSXOXO00_

_ZAFAFA BIYAR PAID NOVELS_

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply