Daudar Gora Book 2 Hausa Novels

Daudar Gora Book 2 Page 49


Daudar Gora Book 2 Page 49
Viral

DAUDAR GORA….!!
Chapter: 49
Kyakykyawan bowl din data dauro saman
tray mai kyau shima da tambulan din madara
yabi da kallo. Ta ajiye a saman dan table din
data janyo kusa da gadon kasancewar a baki-
baki ya ke zaune shi ta daura. Bowl din ta bude
tana dan kallonsa kasa-kasa kamar yanda yake
binta da shegen kallon nan nasa. A saman lips
ta furta “Kana son shi?”. Gasashen naman da ke
ta tashin kamshi mai tada kwadayi ya dan kalla.
Batare da yace komai ba ya kamo hanunta da ke
rike da murfin ya zaresa ya ajiye. Rikota yay ya
zaunar a kusa da shi. “Sai dai in zaki bani da
kanki. Hannuna ciwo suke min”. Yanda yay
maganar acan kasan makoshi matuka ya sata
kallonsa da sauri, ido daya ya kashe mata da
sakar mata wani lalataccen murmushi daya
nema raba jikinta na numfashinta. Da sauri ta
maida kan ta risinar zuciyarta na wani masifar
harbawa da sauri-sauri.
Hannunta ya riko cikin nasa ya dan murza
yana kara narkar da idanunsa kan fuskarta
Cikin sake tausasa harshe da cigaba da murza
hannun ya ce, “A duk lokacin da kike tare da15:37
hannun ya ce, “A duk lokacin da kike tare da
<
an ki kallesa abokin ki, amininki, yaya
A
kal harma kaninki idan ya kama, sannan farin
cikin ki. Ina son gidana da iyalina su kasance
aljannar duniyata da duk inda naje na dawo da
damuwa za’a goge min shi da farin ciki, duk
sanda kaina ya dauka zafi za’a sanyaya min shi
da nishadi. Duk sanda na shigo da farin ciki za’a
tayani yi har ma a ninka min shi da wani da yafi
wanda nake tare da shi. Anan Eshaan sunansa
Eshaan Ion Haysam Abdul-majeed MIJIN
Fhareedah (Iffah) bint Zayyan ba Tajwar Eshaan
ko Shahan-shan ba. Ki raineni kamar jariri a
fadarki, Ni kuma mai sallamawa ne gareki duk
rintsi TAURARUWA TA”.
Wata irin nutsuwa ce ke ratsa mata zuciya,
tabbas tana jin dadin kasancewa da shi, amma
har yanzu bata san mi takeji game da shi ba. Ita
dai kawai yana burgeta, a cikin ado ko sabanin
hakan. Sannan duk da taji ciwo da a jikinta da
jigatuwa a jiya batajin haushinsa ko jin bai
kyauta ba, dan koba komai tayi ilimin addini,
tasan hakkokin mace aka mijinta, tasan
hakkokin miji akan matarsa, tasan muhimmancin
aure da fa’idarsa. Ta kuma san Shahan-shan
bazai taba sakinta ba koda ace zata bukaci
haka. Mammy ta sake tisa mata fiye da abinda
ta sani, har ma da wanda zatayi domin tabbatar
da kanta a matsayin diya MACE a gabansa ko gaban wanin sa
“Wayyo!”.
A
ada yana matse ciki, da sauri ta kalles
yamutse fuska kamar gaske shi adole yunwa
yake ji.
Cike da nuna damuwa ta ce, “Sorry”. Sai
kuma ta dakko tray din saman cinyarta. Cokali ta
dauka zata diba naman ya rike hannun. Kallonsa
ta sakeyi da mamaki. Cikin dan dage gira ya ce,
“Nikam da hannu nake so”. Komai batace ba ta
ajiye cokalin kawai, tare da ajiye trayn ta mike,
bai ta nufa bata wani jima ba ta dawo da alama
hannu ta wanko. Tray din ta sake maidawa
saman kafarta bayan ta koma inda ta tashi ta
zauna ta debo naman ta kai bakinsa. Hannun ya
riko da kyau ya karasa da naman bakinsa yana
lumshe idanunsa, harda sakin siririyar ajiyar
zuciya. Ita sai ma abin ya bata dariya harda
murmusawa.
Wani irin sanyi da nutsuwa yaji har cikin ranta
ganin tayi murmushin. Dan gaba daya yau bakin
ya mutu kamar ba ita ba, shi kuma yafi son yaga
ta saki jiki da shi tana kiriniyarta da surutu
kamar da. Sosai yaci naman har hakan ya bata
mamaki, hakama madaran. A hankali ta rumtse
idanunta sanda yake tsotse yatsun hannun abin
kamar da gayya. Da gayyar kuwa yake yi, dan
yana kallon yanda take faman matse ido yana murmushi a zuciyarsa
Bai bar dakin ba sai da ana kiran sallar magariba
<
. Yace ta shirya kafin ya dawo zata
rakasa wani waje. Da to ta amsa masa kanta a
kasa, dan duk wannan abun da ake bata yarda
su hada ido sai da kuskure. Bayan fitowarsa
alwala a bathroom har ya wuceta ya dawo da
baya, kama ta yay ya mikar tsaye da ga zaunen
da take. Fuskarta ya dago dan taki yarda ta
kallesa, shima bai matsa da sai ta kallesan ba ya
manna ma goshinta sumba mai lafiyar da har sai
da ta sanya jikinta motsawa. Idanunta a rufe har
sai da ya fice sannan ta bude tana sauke
nannauyar ajiyar zuciya, ita har yanzu ta kasa
sabawa da salon nasa sam.
Sai da ta dan kara gasa kanta kamar yanda
Mammy tace ta dinga yi akai-akai sannan tayo
alwala ta fito gabatar da sallar magriba. Bayan
ta idar zama tai tunani mai zurfi akan Tajwar
Eshaan, mutum nan nada abubuwan ban
mamaki boyayyu, tabbas ta yarda hatsabibin
kansa ne kamar yanda su Miran Arshaan ke
fada. Gaskiya tana bukatar sanin yanda akai su
Baby suka kasance a wata kasa bayan su Miran
Jasim sun mata karyar ya kashesu. Kenan video
din data gani jabu ne ko mi?. Rashin amsa da
bukatar samunta ya sata mikewa ta gabatar da
sallar isha’i da ake kira. Bayan ta idar ta shiga
gyara jikinta dan haka kawai take dokin fitar duk
da bata san ina suka nufa ba. Tsaf take cikin bakar doguwar rigar abayar datai mata kyau,sai Ver din nan da in aka nada yake yi kamar baoy
hijab fari. Fitowa tai tsabar zumudin son fitar ta
su. Dakin da suka kwana ta nufa duk da bata
zaton ya isa dawowa salla.
Kusan a tare suka aura hannayensu kan
handle din kofar, ita ta tura shi kuma ya ja batare
da kowanne yasan da dan uwansa ba. Cak ta
tsaya kanta a kasa tana mai rumtse idanunta
dan wata irin kunyarsa takeji har cikin kashinta.
Ga kwarjini mai irin mamaye waje din nan da ya
kara mata. Kusan minti daya suka kwashe a
wajen ita bata tanka ba shima bai ce ba. Tasan
in zasu kwana ma zai iya, dan haka ta dan saci
kallonsa ta gefen ido. A hankali ta janye idanun
nata gain yanda ya kafeta da shegen kallon
nan nasa mai hanata sukuni. Sai ta samu kanta
da in inar fadin, “Barka da dawowa”. Karamar
ajiyar zuciyar da bata ji ba ya yayi a ciki, batare
da ya amsa gaisuwar tata ba ya karasa fitowa,
fuskar babu fara’a sam kamar ko yau she, sai
wani irin kwarjini mai cika idon mai kallo, a fisge
ya furta, “Muje” yana rabata ya wuce cike da
takun nan nasa daddaya. A hankali ta dan sauke
numfashi dan jinta take kamar an daureta a
wajen, sai kuma ta bisa da kallo kasa-kasa tana
mai tsarkake sunan UBANGIJI mahaliccin
wannan kyakykyawar halitta. (Kyau dai kam ALLAH ya bashi, sai dai miskilancin nan da jin
nan da ke zagaye da shi) ta dan nal
fuska kamar zatai magana, sai kuma ta fasa
ranta fal tunanin ina ma zasu je a daren nan?
rashin mai bata amsa ya sata dan zabura tabi
bayansan. Ganin ya nufi lift.. taji duk ta tsure. Ita
dai harga ALLAH abin nan baya wani birgeta.
Dan indai ta shiga sai tayi hajijiya. Shiyyasa ya
zamto sai ta rike wani dan batama taba gigin
shiga ita kadai ba. Jiki a sabule ta shiga, jin
kofar ta rufe kanta ta rumtse idanu da sauri, sai
kuma ta bude akan yatsansa da ke kokarin
danna inda yake bukatar suje. “ALLAH ina jin
toro” ta fada kamar zatai kuka. Sarai ya jita,
amma sai bai nuna yaji ba ya gyara tsaiwarsa
bayan ya danna 2 floor. Iffah da ke jin kamar ta
fasa kuka a hankali tai yunkurin zamewa dan
gara ta zauna zai fi mata sauki. Babu zato taji an
riko mata hannu, kafin ta iya ko bude idanunta
tajita cikin jikinsa da ke fidda wani irin
sirrintaccen kamshi mai ratsa zuciya da bargo
da bazata taba iya mantawa ba. Da sauri ta
bude idanunta sai ko cikin nasa da ke kallonta,
dole ta maida nata ta rufe da sauri zuciyarta na
wani irin bugawa da sauri-sauri, tabbas bazata
mance wannan turaren ba, dan turarene da ta
dinga fafitikar nema a washe grin da aka
dakkota da ga sashenta cikin dare aka maidata
nashi. Kenan da gaske shi dinne ya je ya
dakkota kokuwa yaya akai? Dan wannan Kamshin dai shine. Tsaf ya fahimci inda ta nura,
kuma a randa ta dinga neman turaren ya sani
sarai, abinda bata sani ba ya ajiye abinsa ne
kawai inda bataima zaton ganinsa ba o kawowa
a ranta zai ajiye din.
“Zamu kwana anan ne?”. Ya fada a kasan
makoshi yana kallon kyakykyawar fuskarta da
ke kwance a kan kirjinsa. Idanun ta bude, sai
kuma taja jikinta baya kunya na wani mamayeta.
Dauke idanunsa yay da ga kallonta ya fice,
itama sai ta bisa tana sauke ajiyar zuciya a
jajere, sai kuma ta saki murmushi dan ita da
kanta kunyar kanta taji. Wata hanyar da batama
san da ita a wajen ba suka nufa, koda yake
bawai ta taba shiga wani waje a floor 2 din nan
bane bayan falo, shima a randa Malikat
Haseenat ce ta kawota da suka biyo komai daki-
daki ba kamar yanda yay ba yanzu
Inda suka shigo dinne ya sakata tsayawa
turus tana kallonsa. Sai kuma ta dan waiga ta
kalli hanyar da suka fito, ita fa gaba daya notikan
kanta sun kwace, ta ma rasa ta yanda zata
misalta ta inda wannan hanyar take a zahirin
cikin gidan, dan ita shaidace tsakanin sashensa
da na Malikat Bushirat akwai nisa. Duk da sunyi
yar tafiya suma amma sai gasu cikin sauki.
Kallonsa tai fuska a marairaice kamar ba Iffah’r
nan matsiwaciya ba da ya sani ta ce, “ALLAH toro nake ji”. Kallonta yake da shanyayyun
idanun nan nasa masu kaifi kamar bazaice
komai ba, sai kuma jitai a hankali kamar mai
rada ya furta, “Nima tsoron nake ji ai”. Idanu ta
dan waro alamar mamaki tace, “Kai din?”. Kansa
ya dan kada mata da lumshe idanunsa ya bude
duk a lokaci daya. Sai kuma ya kai hannunsa kan
nata ya matsota jikinsa. “Ki karamin karfi”. Ya
fada yana rungumeta cikin jikin nasa.
Daburcewa tai ma ita gaba daya. Tai kokarin
dagowa ya hana hakan. Dole ta hakura tai luff
tana mai shakar kamshin da jikinsa ke fitarwa
mai azabar dadi. Kusan minti biyu suka kwashe
a wajen kafin ya dagota a hankali, kin yarda tai
su hada ido sam, shima sai bai matsa ba ya ja
hanunta kawai yana dan murmushin da iyakarsa
makoshi suka shige.

Leave a Comment





No one has commented yet. Be the first!
Leave a Reply